An Nada Shugaban Hukumar Fasahar Sadarwa Da Inganta Tattalin Arziki Ta Jihar Jigawa
Published: 4th, April 2025 GMT
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da nadin Dr. Mohammed Hassan a matsayin Darakta Janar na farko na Hukumar Fasahar Sadarwa da inganta Tattalin Arzikin ta fasahar zamani ta Jihar Jigawa.
Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ya fitar a Dutse.
Kafin nadin nasa, Dr. Muhammad Hassan shi ne shugaban hukumar Fasahar Sadarwa da Kimiyya ta Jigawa, wato Galaxy ITT.
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa sabo shugaban hukumar ya sami digirinsa na farko a fannin Lissafi daga Jami’ar Bayero, Kano, a shekarar 2008. Daga bisani, ya samu digiri na biyu a fannin Kimiyyar Kwamfuta daga Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Afirka (AUST), Abuja, a shekarar 2011, sannan ya ci gaba da karatu har ya samu digirin digirgir (Ph.D) a fannin Kimiyyar Kwamfuta da Injiniyanci daga Jami’ar Aizu da ke kasar Japan, a 2018.
Haka nan, Gwamnan ya amince da naɗin Baffajo Beita a matsayin sabon shugaban Galaxy ITT.
Kafin naɗinsa, Beita Babban Jami’in Bayanan Fasaha ne a Galaxy Backbone da ke Abuja. Yana da ƙwarewa mai zurfi a fannin fasahar sadarwa, musamman a tsarin gudanar da cibiyoyin sadarwa, tsaro na yanar gizo, da ƙirƙirar fasahar yanar gizo.
Beita ya kammala digirinsa na farko a fannin Kwamfuta daga Jami’ar Anglia Ruskin, kuma ya fara aikinsa ne a Makarantar Informatics ta Jihar Jigawa da ke Kazaure, kafin ya taka muhimmiyar rawa a manyan ayyukan fasahar sadarwa a Turai, Gabas ta Tsakiya, da Afirka (EMEA) a fannoni daban-daban, ciki har da masana’antar mai da gas, da sarrafa kayayyaki, da harkokin kuɗi”.
Bugu da ƙari, Gwamnan ya amince da naɗin Muhammad Nura Zubairu a matsayin Daraktan Zartarwa na Ayyukan Fasaha, da Umar Ibrahim Gumel a matsayin Daraktan Zartarwa na Harkokin Kasuwanci a Galaxy ITT.
Kafin wannan matsayi, Muhammad Nura ya kasance Injiniyan Tallafin Sadarwa a Galaxy ITT, kuma ya kammala babbar difloma (HND) a fannin Tattalin Arzikin Hadin Gwiwa da Gudanarwa daga Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kano a shekarar 2010.
“Wadannan muhimman nade-nade na cikin shirye-shiryen Gwamna Namadi na ƙarfafa tattalin arzikin Jihar Jigawa ta fasahar zamani, domin tabbatar da cewa hukumar na da kwararrun shugabanni da za su jagoranci kirkire-kirkire da inganta ayyukan fasahar sadarwa a ciki da wajen jihar” in ji SSG.
Malam Bala Ibrahim ya ƙara da cewa an zaɓi waɗanda aka naɗa ne bisa cancanta, ƙwarewa, da nagarta.
Ya bukaci dukkan waɗanda aka naɗa da su yi aiki tukuru don aiwatar da manufofi da shirye-shiryen gwamnati bisa kyakkyawan.
Sanarwar ta ƙara da cewa, dukkan waɗannan nade-naden sun fara aiki ne nan take.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Fasahar Sadarwa Jigawa fasahar sadarwa Jihar Jigawa daga Jami ar
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin Bana: Kamfanoni 4 da za su yi jigilar maniyyata — NAHCON
Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta sanar da soma jigilar maniyyatan bana zuwa Saudiyya daga ranar 9 ga watan Mayu yayin da take tabbatar da kammala shirye-shirye aikin Hajjin bana.
Hukumar ta bayyana hakan ne bayan wata ganawa da shugabanta da wakilan majalisar gudanarwa suka yi da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima.
An daƙile yunƙurin juyin mulki a Burkina Faso Abubuwa 5 da ya kamata ku sani kan mutuwar Fafaroma FrancisMataimakin shugaban kasar ne ya gayyaci shugaban hukumar, Farfesa Abdullah Saleh Usman da wakilan sashen gudanarwa zuwa ganawar a ofishinsa domin sanar da shi inda aka kwana game da shirye-shiryen aikin hajjin.
“Mun yi masa bayani game da shirye-shiryenmu a Makkah da Madina da Arafa kuma ya gamsu, har ma ya ba mu umarnin yadda za mu haɗa kanmu mu yi aikin har zuwa ƙarshensa.”
Kazalika, shugaban ya ce suna sa ran kammala aikin kwashe maniyyatan a ranar 24 ga watan Mayu.
Hukumomi sun ce mutum 43,000 ne za su je aikin Hajjin daga Nijeriya a wannan shekara yayin da a bara mutum kusan 95,000 ne suka yi ibadar.
“A shekarar da ta wuce muna da alhazai 95,000, kamfonin jigila uku muka bai wa aiki. Yanzu da muke da alhazai 43,000, mun ɗauki kamfonin huɗu. To ina maganar ƙarancin jirage a nan?,” in ji farfesan.
Bayanai sun ce kamfonin sufurin jiragen da za su yi jigilar maniyyatan sun hada da Airpeace — 5,128 da Flynas — 12,506, sai Max Air — 15,203 da kuma Umza Air — 10,163.
A ’yan makonnin nan ne ’yan majalisar gudanarwar hukumar suka rubuta wa Kashim Shettima koke, suna zargin shugaban NAHCON, Farfesa Abdullah Saleh da mayar da su saniyar ware wajen gudanar da lamurran hukumar, zargin da shugaban ya musanta.
Hotunan ganawar wakilan NAHCON da mataimakin shugaban kasa: