Aminiya:
2025-04-25@04:34:28 GMT

Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasu

Published: 4th, April 2025 GMT

Fitaccen malamin addinin Islama da ke Jihar Bauchi, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi ya riga mu gidan gaskiya.

Almajiransa sun tabbatar wa Aminiya cewa ya rasu ne a gidansa da ke Bauchi inda za a yi jana’izarsa a safiyar wannan Juma’ar.

Malamin ya yi fama da rashin lafiya inda gabanin watan Ramadana ya fita neman magani a ƙasashen Masar da Saudiyya.

Fitowarsa ta ƙarshe ita ce ranar Idin ƙaramar Sallah da ta gabata, inda ya yi huɗuba kan muhimmanci haɗin kai a tsakanin musulmi.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba

Kujeru dubu daya da dari hudu da bakwai ne aka ware wa hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Taraba domin maniyyata bana.

 

Babban Sakataren Hukumar mai barin gado Umar Ahmed Chiroma ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan matakin da ake na shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin bana na 2025 ba tare da tangarda ba.

 

Aikin Hajji daya ne daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar kuma Musulmin muminai na gudanar da aikin Hajji a kowace shekara akalla sau daya a rayuwarsu.

 

Chiroma ya ce hukumar ta kai wani mataki na ci gaba ta fannin shirye-shirye kamar yadda hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta bayar, inda ya ce sama da maniyyatan jihar 500 ne suka kammala biyan kudadensu.

 

Alhaji Ahmed Umar Chiroma ya kara da cewa a halin yanzu sama da Alhazai dubu biyar ne suka biya kudin aikin Hajji, yana mai kira ga sauran maniyyatan da su gaggauta biya domin cika wa’adin da hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kebe.

 

Ya yi bayanin cewa hukumar ta samu karancin masu zuwa aikin hajjin ba, inda ya danganta hakan ga tabarbarewar tattalin arziki ganin yadda amfanin gona da shanu suka ragu matuka a farashi.

 

Sakataren zartarwa ya bayyana manoma da makiyaya a matsayin manyan masu biyan kujerun aikin Hajji a jihar, inda ya nuna cewa gwamnatin jihar ta biya kujeru hamsin (50).

 

Chiroma ya ci gaba da bayyana cewa nan ba da dadewa ba hukumar za ta fara yin alluran rigakafi da tantance maniyyatan da ke shirin kammala shirye-shiryen aikin Hajji.

 

A cewarsa, hukumar ta kammala shirye-shirye a sansanin Alhazai a Jalingo, babban birnin jihar.

 

Sakataren zartarwa mai barin gado ya bayyana karara cewa jami’an hukumar sun ziyarci kasar Saudiyya inda suka samu masaukin da suka dace da mahajjatan jihar Taraba.

 

Umar Ahmed Chiroma ya yabawa Gwamna Agbu Kefas bisa daukar nauyin Alhazai hamsin, yana mai jaddada cewa wannan karimcin zai taimaka matuka wajen taimakawa mutane da dama wajen gudanar da aikin hajjin 2025.

 

 

Sani Sulaiman

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • 2025: NAHCON Ta Ware Kujerun Aikin Hajji 1,407 Ga Jihar Taraba
  • Dalilin Da Zai Iya Hana Ni Sake Bugawa Manchester United Wasa – Rashford
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi
  • Manchester United Na Zawarcin Matheus Cunha Na Wolves
  • Iyalen Surajo Malumfashi na Radio Nigeria Kaduna Yana Gayyatar Jama’a Zuwa Daurin Auren ‘Yar Sa
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • 2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana
  • An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tube a cikin daki