HausaTv:
2025-04-25@08:04:19 GMT

Kisan ma’aikatan ceto : MDD ta gargadi Isra’ila game da aikata laifin yaki

Published: 4th, April 2025 GMT

Kwamishinan kare hakkin dan Adam na Majalisar Dinkin Duniya ya gargadi Isra’ila game da harin da ya yi sanadin mutuwar ma’aikatan ceto a Gaza yana mai cewa hakan zai iya kasancewa ‘lafin yaki’. Ma’aikatan agaji 15 ne suka ras arayukan a wani kazamin hari da Isra’ila ta kai kan motocin daukar marasa lafiya a Gaza wada ya fiddo a fili irin ” laifuffukan yaki da sojojin Isra’ila suka kwashe tsawon lokaci suna aikatawa a zirin Gaza”.

Kafin hakan dama hukumar kula da hakkin bil adama ta MDD ta amince da kudurin dake kira ga Isra’ila da kada ta aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.

An amince da kudurin ne ranar Laraba yayin taron hukumar na 58, bayan ya samu kuri’un amincewa 27 da na kin amincewa 4, kana kasashe 16 sun kaurace wa kada kuri’ar.

Kudurin ya kuma bayyana takaici game da keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da Isra’ila ta yi, tare da yin kira da ta sauke nauyin dake wuyanta.  

Har ila yau, kudurin ya soki yadda Isra’ila ta yi amfani da yunwa a matsayin wata dabara ta yaki a Gaza, da hana samar da agajin jin kai da kawo tsaiko ga samar da kayayyakin agaji da hana fararen hula abubuwan da suke bukata na rayuwa, kamar abinci da ruwa da lantarki da makamashi da hanyoyin sadarwa.

Ya kuma bayyana damuwa matuka game da kalaman jami’an Isra’ila da ka iya ingiza kisan kiyashi, inda ya bukaci Isra’ila ta sauke nauyin dake wuyanta bisa doka na kare aukuwar kisan kiyashi.

Bugu da kari, kudurin ya gabatar da wasu jerin bukatu ga Isra’ila, ciki har da tabbatar da samar da agajin jin kai ba tare da tangarda ba da gaggauta dawo da tsarin samar da muhimman kayayyakin bukata ga Palasdinawa a Gaza da ba Palasdinawan da suka rasa matsugunansu damar komawa dukkan yankunan zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya

A ranar 17 ga watan Afrilun da muke ciki ne wakilai ko ministocin noma na kasashen kungiyar BRICS suka taro a Brazilian a kasar Brazil inda suka rantaba hannu kan shelanta shirin namusamman na bunkasa ayukan noma da kuma harkokin samar da abinci da kuma wadatar da shi ga kasashen duniya farko ga kasashen kungiyar.

Shirin dai ya hada da na shekara ta 2021-2024 da kuma na 2025-2028, wadanda kungiyar zata aiwatar da su tare.

Shirin ya hada da bunkasa ayyukan noma da samar da wuraren ajiye kayakin noma da kuma taimakawa kananan ayyukan noma a kasashen kungiyar saboda smaar da manoma wadanda zasu yi noma mai yawa nan gaba. Sannan rage abubuwan da ke hana ayyukan noma ci gaba a cikin kasashen kungiyar .

Kasashen kungiyar BRICS dai suna da kasha 54.5 % na yawan mutane a duniya, sannan suna noman 1/3 na filayen noma a duniya, wanda zai bada damar aiwatar da dukkan wadannan ayyuka da sauki da kuma sauri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Mutum 7 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Fyaɗe Da Kashe Budurwa A Bauchi
  • **Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba
  • Gwamnatin Siriya Tana Daukan Matakan Matsin Lamba Kan Gwagwarmaya Domin Samun Yardan ‘Yan Sahayoniyya
  • Tallafa Wa Al’umma: Ya Dace Gwamnoni Su Yi Koyi Da Jihar Zamfara – UNDP
  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • Hezbollah, ta yi tir da Isra’ila kan kisan gillar da aka wani babban jigonta
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan