Iran ta yi kira ga kungiyar Shanghai ta yi Allah wadai da barazanar Trump
Published: 4th, April 2025 GMT
Jamhuriyar Musulinci ta Iran ta yi kira ga kasashe mambobi kungiyar hadin guiwa ta Shanghai da ta yi Allah wadai da barazanar Trump ta baya baya nan kan kasar.
A taron ministocin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai da aka gudanar a birnin Moscow a ranar Alhamis, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran Majid Takht Ravanchi, ya yi kira ga mambobin kungiyar SCO da su yi Allah wadai da kalaman da shugaban na Amurka Donald Trump ya yi a baya-bayan nan kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, lamarin da ya ce yana da hadari.
Majid Takht Ravanchi ya yi kakkausar suka ga barazanar harin bam da Trump ya yi a wata hira da tashar NBC News, inda ya ce, hakan ya keta dokokin kasa da kasa, da kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya wanda ya haramta amfani da karfi karara a kan iyakokin kasa da ‘yancin kai.
Takht Ravanchi ya bayyana cewa Iran ta bukaci kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya yi Allah wadai da wannan hali da ba za a amince da shi ba tare da daukar matakan da suka dace don kiyaye zaman lafiya da tsaron kasa da kasa.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya sake jaddada matsayar kasar Iran da cewa duk wani yunkuri daga Amurka zai fuskanci mai da martani cikin gaggawa.
Ya yi kira da a fitar da sanarwar hadin gwiwa ta SCO da ke yin Allah wadai da barazanar Amurka tare da yin kira ga kwamitin sulhun da ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa na wanzar da zaman lafiya da tsaro a duniya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: yi Allah wadai da
এছাড়াও পড়ুন:
Iran za ta karbi bakuncin taron farko kan kare hakkin dan Adam a Gabas ta tsakiya
Jamhuriyar Musulinci ta Iran, za ta karbi bakuncin taron farko na kasa da kasa kan kare hakkin bil adama a Gabas ta Tsakiya.
Shugaban Hukumar Al’adu da Sadarwa ta Musulunci Mohammad Mehdi Imanipour ya bayyana cewa, za a gudanar da taron farko na kasa da kasa kan batun kare hakkin bil’adama kan Gabas ta Tsakiya a lokaci guda a Tehran, Qom da Isfahan daga ranar 28 ga Afrilu zuwa 2 ga Mayu.
Hakkin dan adam na daya daga cikin batutuwan da suka fi muhimmanci a cikin al’ummomi, saidai a baya bayan nan wasu gwamnatoci sun yi watsi da yancin dan adam gaba daya.
Mohammad Mehdi Imanipour ya ce “A yau, misali karara na take hakkin bil’adama shi ne kisan kiyashi da ake yi a Gaza.”
Ya ce Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana da abubuwa da dama da za ta iya fada a fagen kare hakkin bil’adama, don haka ta kai ga gayyatar wasu kasashe a wannan taro domin neman kafa kawancen kare hakkin bil’adama na duniya mai sabon salo.
An aika gayyata a hukumance ga kasashem duniya 32 da kuma manyan cibiyoyin kimiyya da ilimi 36 dake hadin gwiwa tare da taron.