Aminiya:
2025-04-26@01:29:56 GMT

Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike

Published: 4th, April 2025 GMT

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ya yanke jiki ya faɗi har aka kai shi asibiti a ƙasar waje.

Ya ce wannan ƙarya ce da maƙiyansa na siyasa suka ƙirƙira don kawar da hankalin mutane.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasu

Wike, ya yi wannan bayani ne a Abuja a ranar Alhamis yayin da ya kai ziyara wajen wani aiki da ake shirin ƙaddamarwa a watan gobe domin bikin cikar Shugaba Bola Tinubu shekara biyu a mulki.

A wata sanarwa da daraktan yaɗa labaransa, Anthony Ogunleye, ya fitar, Wike ya ce waɗanda ke yaɗa wannan labari suna ƙoƙarin juyar da hankalin jama’a daga batun da tsohon shugaban ma’aikatan Jihar Ribas ya fallasa na yunƙurin saka bam a majalisar dokokin jihar da kuma hari kan kadarorin gwamnati.

“Babu inda na yanke jiki na faɗi, balle har a fitar da ni zuwa ƙasar waje.

“Ko a ranar da Shugaba Tinubu ya yi buɗa-baki kan zagayowar ranar haihuwarsa na halarta.

“Haka kuma, a ranar Sallah na jagoranci mazauna Abuja zuwa taya shi barkar da sallah. Ba zan damu da irin waɗannan jita-jitar siyasa ba, kuma ba za su hana ni aiki ba,” in ji Wike.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: karya Siyasa yanke jiki

এছাড়াও পড়ুন:

An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace

Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta kama wasu mata biyu a lokacin da suke yunƙurin sayar da wani yaro ɗan shekara huɗu da aka yi garkuwa da shi a Owerri kan kuɗi Naira miliyan 2.7.

An yi garkuwa da yaron ne a Abuja a lokacin da yake tallan kayan miya, sannan aka kawo shi Owerri a sayar da shi kafin a sa’ar kuɓutar da shi daga masu son sayar da shi.

An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji

Waɗanda ake zargin sun haɗa da Joy Ugwu daga garin Idah ta jihar Kogi, da Rosella Michael daga garin  Zamba da ke Abuja, yayin da ta ukun da ake zargin ma’aikaciyar jinya ce da ta tsere a yanzu.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Henry Okoye ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

Okoye ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a Owerri, babban birnin jihar a ranar 14 ga watan Afrilu, biyo bayan wani samame da jami’an tsaro suka yi a lokacin da suke ƙoƙarin siyar da yaron kan kuɗi Naira miliyan 2.7.

Ya ce, an kama mutanen ne biyo bayan ƙoƙarin haɗin gwiwa tsakanin rundunar ’yan sandan Jihar Imo da hedikwatar ’yan sandan shiyya ta 7 da ke Abuja, duk da cewa an miƙa waɗanda ake zargin zuwa sashin binciken manyan laifuka na shiyyar Abuja, domin ci gaba da bincike da gurfanar da su gaban kuliya.

Okoye ya ce, “Rundunar ’yan sandan Jihar Imo ta gano wani mutum da ake zargi da safarar ƙananan yara, lamarin da ya kai ga cafke wasu mata biyu da ake zargi tare da kuɓutar da wani yaro ɗan shekara huɗu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
  • An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna
  • Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe
  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
  • Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira A Ranar Juma’a A Maiduguri
  • Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam
  • An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • Tinubu ya gana da shugabannin tsaro a Abuja
  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar