Aminiya:
2025-04-25@06:07:31 GMT

Hakeem Baba-Ahmed ya yi murabus daga gwamnatin Tinubu

Published: 4th, April 2025 GMT

Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya yi murabus daga matsayin mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa.

Majiyoyi daga fadar shugaban ƙasa sun tabbatar da cewa ya aike da takardar murabus ɗinsa kimanin makonni biyu da suka wuce, inda ya ce dalilansa na ƙashin kai ne.

Batun na yanke jiki na faɗi ƙarya ce — Wike NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta

Har yanzu ba a tabbatar da ko fadar shugaban ƙasa ta amince da murabus ɗin ba.

An naɗa Baba-Ahmed a watan Satumban 2023 a matsayin mai bai wa mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, shawara kan harkokin siyasa.

A lokacin da yake riƙe da muƙamin, ya wakilci gwamnati a taruka da dama na ƙasa da na siyasa.

Sai dai ya sha suka a shekarar 2024, bayan da ya samu saɓani da Ƙaramin Ministan Harkokin Tsaro, Bello Matawalle, kan kalaman da suka shafi Ƙungiyar Tsofaffin Shugabannin Arewa (NEF), inda ya taɓa zama kakakinta kafin naɗinsa.

“Sukar NEF da Matawalle ya yi bai dace ba. Ya fi dacewa ya bayyana irin gudunmawar da ministocin Arewa da sauran jami’an gwamnati irina ke bayarwa wajen inganta tsaro da rage talauci a yankin,” in ji Baba-Ahmed

Matawalle ya mayar da martani da cewa: “Dukkanin wanda Shugaba Tinubu ya naɗa, ciki har da Dokta Baba-Ahmed, na da alhakin kare da kuma tallata ayyukan wannan gwamnati a fannoni daban-daban.”

Baba-Ahmed wanda ya taɓa zama Shugaban Ma’aikata na tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Bukola Saraki, sananne ne wajen tsayawa kan gaskiya da adalci a harkokin ƙasa.

Kafin naɗin nasa, ya kasance Daraktan Yaɗa Labarai na ƙungiyar dattawan Arewa.

Tsohon babban jami’in gwamnati ne daga Jihar Kaduna kuma sananne ne a matsayin dattijo mai kishin Arewa.

Murabus ɗinsa ya jawo ce-ce-ku-ce musamman a tsakanin masu bibiyar al’amuran siyasa a Arewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnatin tinubu Murabus Siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugaban Tsaro Da Ribadu Kan Kashe-kashen Rayuka

Matsalar tsaro ta kara tabarbare a jihohin Filato da Benuwai, inda rahotanni ke cewa, wasu da ake zargin makiyaya ne daga kasashen waje ne ke kai hare-haren kashe rayuka da kuma raba al’umma da matsugunansu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta amince ta bai wa mahajjata kuɗin guzirinsu a hannu
  • **Gwamnati Za Ta Kwace Gidajen Ma’aikatan Da Suka Yi Ritaya Ba Su Biya Bashin Gidaje Ba
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • 2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  • Tinubu ya gana da shugabannin tsaro a Abuja
  • Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugaban Tsaro Da Ribadu Kan Kashe-kashen Rayuka
  • Gwamna da jiga-jigan siyasa a Delta sun fice daga PDP zuwa APC
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • Nda-Isaiah Ta Yaba Wa Matar Shugaban Kasa Tinubu Kan Soyayya Da Tallafawa Talakawan Nijeriya