Aminiya:
2025-04-25@07:46:21 GMT

APC ta ƙaryata jita-jitar sauya Shettima kafin zaɓen 2027

Published: 4th, April 2025 GMT

Jam’iyyar APC, ta musanta jita-jitar cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, na shirin sauya Mataimakinsa, Kashim Shettima, kafin zaɓen 2027.

Jam’iyyar ta ce babu wata matsala tsakaninsu kuma maganar sauya Shettima ba ta da tushe.

Hakeem Baba-Ahmed ya yi murabus daga gwamnatin Tinubu Fitaccen malami Dokta Idris Dutsen Tanshi ya rasu

Daraktan Yaɗa Labarai na Jam’iyyar APC na Ƙasa, Alhaji Bala Ibrahim, ya shaida wa Aminiya cewa wasu ne ke yaɗa wannan jita-jitar don tayar da ƙura.

“Wannan jita-jita ce kawai marar tushe. Maganganu ne da bai kamata a ɗauke su da muhimmanci ba,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, “Ko da a ce akwai wani dalili da zai sa shugaban ƙasa ya sauya mataimakinsa, ba zai iya yin hakan shi kaɗai ba. Dole sai da shawarwari tare da masu ruwa da tsaki.”

Ko da yake APC ba ta bayyana aniyar Tinubu na sake yin takara a karo na biyu ba, magoya bayansa da wasu shugabannin jam’iyya sun fara neman goyon baya don ya sake tsayawa takara a 2027.

Wasu na ganin ya cancanci ya nemi wa’adi na biyu domin kammala ayyukan da ya fara.

A halin yanzu, wasu ’yan siyasa daga yankin Arewa ta Tsakiya suna kira da a ba su tikitin shugaban ƙasa ko mataimaki a zaɓe mai zuwa.

Sun ce tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a 1999, yankin bai taɓa samun shugaba ko mataimakin shugaban ƙasa ba.

Farfesa Nghargbu K’tso, wanda ya wakilci tawagar, ya ce: “Daga cikin yankuna shida na ƙasar nan, Arewa ta Tsakiya da Kudu Maso Gabas ne kaɗai ba su taɓa samar da shugaban ƙasa ko mataimaki ba cikin shekaru 26 da suka gabata. Lokaci ya yi da za a yi adalci da haɗin kai.”

Sai dai Bala Ibrahim, ya mayar da martani cewa buƙatar Arewa ta Tsakiya ba ta da tushe kuma “ta mutu tun kafin ta fara.”

Ya ce yankin bai taka gagarumar rawa a zaɓen da ya gabata ba bare ya nemi irin wannan buƙata, kuma ba yanzu ne lokacin tattauna rabon muƙamai ba, tunda Tinubu bai kammala wa’adinsa na farko ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sauya Mataimaki Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa talauci a Najeriya zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari a cikin shekaru biyar masu zuwa, ciki har da shekarar zaɓe ta 2027.

Wannan hasashe yana ƙunshe ne a cikin rahoton Bankin wanda aka fitar a lokacin taron bazara na Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da ake yi a birnin Washington, D.C., a ƙasar Amurka.

Rahoton ya jaddada cewa duk da wasu nasarorin da aka samu a harkokin tattalin arziki a kwanakin baya, musamman a ɓangaren da ba na man fetur ba a cikin rubu’i na ƙarshe na shekarar 2024, matsalolin da suka shafi dogaro da albarkatun ƙasa da kuma raunin ƙasa na iya kawo cikas ga ci gaba.

A cewar Bankin Duniya, Najeriya, tare da wasu ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni a yankin kudu da Sahara, za su fuskanci ƙaruwar talauci —saɓanin ƙasashen marasa arzikin albarkatu, waɗanda ake tsammanin za su samu raguwar talauci cikin sauri.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

Rahoton ya bayyana cewa, “Ana hasashen talauci zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari tsakanin 2022 zuwa 2027a ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni—ciki har da manyan masu tattalin arziƙo kamar Najeriya da Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango.”

A halin da ake ciki, Sanatan da ke wakiltar Ondo ta Kudu, Jimoh Ibrahim, ya yi kira ga ƙasashen a Afirka, Bankin Duniya, da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da su ba da fifiko ga amfani da bayanai don ci gaban Afirka.

Da yake magana a yayin taron bazara na IMF/Bankin Duniya a Washington, D.C., Amurka, Sanata Jimoh Ibrahim ya jaddada muhimmancin bayanai a ci gaban tattalin arziki da siyasa.

Ya ce, “Idan babu bayanai ba, babu wanda zai iya rage aikata laifuka yadda ya kamata ko kuma gudanar da gwamnatin da ke da nufin cimma nasarar rage talauci.”

Ya ƙara da cewa, “Bayanai kan yawan jama’a da cikakkun bayanai na mutane sun nuna cewa ya kamata ’yan ƙasa su mallaki fasfo na tantancewa domin tattara muhimman bayanai game da su wane ne su da kuma abin da suke yi.”

Sanatan ya yi gargadi ga IMF game da yin hasashe ba tare da ingantattun bayanai ba, yana mai cewa irin waɗannan hanyoyin ba su da inganci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya
  • 2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  • Tinubu ya gana da shugabannin tsaro a Abuja
  • Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugaban Tsaro Da Ribadu Kan Kashe-kashen Rayuka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Hajjin 2025: Kashim Shettima Ya Jinjinawa Hukumar Alhazai Bisa Matakan Da Ta Dauka
  • Nda-Isaiah Ta Yaba Wa Matar Shugaban Kasa Tinubu Kan Soyayya Da Tallafawa Talakawan Nijeriya
  • Shettima Ya Gayyaci Shugaban NAHCON Da Mambobin Hukumar Kan Shirye-shiryen Hajjin 2025
  • 2027: Fastocin Takarar Shugaban Ƙasa Na Gwamnan Bauchi Sun Bayyana