Wata Babbar Kotu A Seoul Ta Tube Shugaban Kasa Daga Mukaminsa Saboda Doka Ta Bacin Da Ya Kafa
Published: 4th, April 2025 GMT
Kotun kare kundin tsarin mulki a kasar Korea ta Kudu ta tabbatar da tsige shugaban kasa Yoon Suk Yeol daga kan kujerar shugabancin kasar a safiyar yau Jumma.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto alkalan kotun koli na kare kundin tsarin mulkin kasar, su 6 suna karanta wannan hukuncin da suka yanke kan tsahoin shugaban.
Kafin haka dai Yeol lauya ne wanda ya shiga harkokin siyasa a yan shekarun da suka gabata, sannan ba zata ya lashe zaben zama shugaba a shekara ta 2022. Amma a shekarar da ta gabata wato 2024 ya kafa doka t abaci a kasar saboda kare kansa da matarsa daga wasu kura kurai da suka aikata. Wannan dokar day a kafa ya rikita harkokin siyasa a kasar na wani lokaci.
Wanda ya kai ga majalisar dokokin kasar ta tubeshi daga kan kujerar shugabancin kasar. Amma daya baya kotun kundin tsarin mulkin kasar ta dauki alhakin duba cikin lamarin. Inda daga karshe ta tabbatar da tube shi a safiyar yau Juma’a.
Kafin haka dai a jibge jami’an tsaro kan manya-manyan titunan birnin seoul don hana duk wani tashin hankali dangane da hukuncin da kotun zata yanke.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede, ya ba wa dakarun rundunar wa’adin wata guda su fatattaki sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta Mahmud a da ta ɓulla a Jihar Kwara.
Oluyede ya ba da wannan umarnin ne a lokacin da yake jawabi ga sojojin a ziyarar da ya kai Barikin Sobi da ke Ilorin, babban birnin jihar.
“Daga wata mai zuwa, ba na son in ƙara jin mostin waɗannan ’yan ta’addan a yankin Dam ɗin Kainji,” in ji babban hafsan sojin.
Ya umarce su da su kawar da ’yan ta’addan daga ƙananan hukumomi biyun da suka addaba, yana mai jaddada cewa yana son a kammala aikin cikin wata mai zuwa.
Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa gidan rediyo na haɗin gwiwa NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka KasuwanciBabban hafsan sojin ya ce Najeriya ba za ta iya ba da damar ’yan fashin daji ko ’yan ta’adda su ƙara yaɗuwa zuwa wani ɓangare na ƙasar ba.
“Don haka, kuna nan kuma na san za ku yi hakan don tabbatar da cewa waɗancan mutanen sun bar mana wannan wurin,” kamar yadda ya shaida wa sojojin.
“Idan suna son shiga wata ƙasa, wannan su ta shafa, amma dole ne ku kawar da su daga waɗannan dazuzzukan don kada mu sake samun wata ƙungiyar Boko Haram da za ta dame mu a nan.
“Ina iya gaya muku, cikin wata mai zuwa, al’amura za su bambanta. Abin da ke faruwa a Kwara ba zai iya yin barazana ga zaman lafiyar Najeriya gaba ɗaya ba; lamari ne keɓantacce kuma za mu magance shi kai tsaye.”