Gwamnati Za Ta Dawo Da Sayar Wa Dangote Ɗanyen Mai Da Farashin Naira
Published: 4th, April 2025 GMT
Da yake tofa albarkacin bakinsa kan sayar da danyen mai da naira, wani babban jami’in gwamnati wanda ke da masaniya sosai kan lamarin da ke aiki da kwamitin da aka kafa don shirin ya bayyana cewa gwamnati ba wai ta dakatar da tsarin bane gaba daya.
“Shirin cinikayyar danyen mai a kan naira zai ci gaba saboda na gano cewa tsarin ya yi tasiri sosai ba kawai a kan farashin mai ba, har ma da kyautata ci gaban tattalin arziki.
“Bugu da kari, kwamitin yana jiran hukumar da ke kula da harkokin man fetur ta Nijeriya ta gabatar da rahoton aikin da aka ba ta dangane da wannan manufar. Da zarar an yi haka, abu na gaba shi ne a duba abun da za a yi na gaba kan wannan batun hada-hadar mai da kudin naira,” cewar majiyar wanda ya nemi a dakaye sunansa.
Idan za a tuna dai, a ranar 1 ga watan Oktoban 2024 ne gwamnati ta fara sayar da danyen mai a kan naira ga matatar man dangote domin inganta samar da man fetur, lamarin ya kai ga taimaka wa kasar nan da samun rarar miliyoyi na dala da take narkawa wajen sayo danyen mai daga kasashen waje, kuma shirin ya taimaka sosai wajen samun ragi kan farashin fetur.
A baya-bayan nan, kakakin kamfanin NNPC, Olufemi Shoneye yayin da ke fashin karin haske kan batun karewar hada-hadar cinikin, inda ya ce, “Bari na fayyace wannan lamarin, daman an kulla yarjejeniya ce na watanni shida, ya danganci wadatar danyen mai, kuma zai kare ne a karshen watan Maris na 2025.
“Tattaunawa na ci gaba da gudanar kan yadda za a kulla sabuwar yarjejeniya.
“A karkashin wannan yarjejeniyar, NNPC ya samar da danyen mai sama da ganga miliyan 48 ga matatar dangote tun watan Oktoban 2024.
“A takaice, NNPC ya samar da danyen mai ganga miliyan 84 ga matatar tun lokacin da ta fara aiki a shekarar 2023.
“NNPC ya himma wajen samar da danyen mai ga matatun mai na cikin gida a bisa tsarin yarjejeniya da sharuddan da aka cimma,” ya shaida.
Kazalika, rahoton S&P ya nuna cewa matatar mai ta dangote ta sayo danyen mai na farko ne daga kasar Burazil da Ekuatorial Guinea.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Naira
এছাড়াও পড়ুন:
An fara raba wa almajirai tabarma da gidan sauro a Yobe
Hukumar Ilimin Larabci da Musulunci ta Jihar Yobe (AISEB) ta fara rabon tabarmi da gidajen sauro ga almajirai a fadin jihar.
Sakataren Zartarwa na hukumar, Malam Umar Abubakar ya cen tabarmi da gidajen sauron tallafi na daga cikin kokarin da gwamnati ke yi na inganta walwala da rayuwar almajiran makarantun tsangaya a fadin jihar.
A cewarsa, shirin ya yi daidai da umarnin da gwamnatin jihar ta ba hukumar na tabbatar da kulawa da kuma tallafa wa yara almajirai.
Ya bayyana cewa an tsara rabon ga ɗalibai 100 a kowace karamar hukuma cikin kananan hukumomin Jihar 17, wanda za a fara daga makarantun Goni Yahaya da Goni Muhammad Tsangaya da ke Damaturu.
Ya ƙara da cewa, kayayyakin za su taimaka wa almajirai su kasance da cikin tsafta da walwala, kuma hukumar za ta ƙara kaimi wajan samar da abubuwa kamar su ciyarwa, sutura, da samar da kayayyakin koyo da koyarwa.
A nasa jawabin godiya, shugaban makarantar Goni Muhammad Tsangaya Malam Goni Muhammad ya bayyana tallafi a matsayin wanda ya dace, kuma zai iya canza rayuwar almajiran, yana mai kira ga ƙungiyoyi da ɗaifaikun mutane da su yi koyi da irin wannan matakin.
“Hakan zai taimaka matuƙa wajen inganta rayuwar ɗalibanmu, musamman wajen hana kamuwa da cututtuka da sauro ke haifarwa da kuma samar da kwanciyar hankali yayin barci,” in ji shi.
Ana sa ran ci gaba da rabon kayayyakin nan da makonni masu zuwa a dukkan kananan hukumomin jihar 17.