Leadership News Hausa:
2025-04-25@08:11:54 GMT

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

Published: 4th, April 2025 GMT

De Bruyne Zai Bar Manchester City A Ƙarshen Kakar Wasanni

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, ya ce: “Ko muna so ko ba mu so, lokaci ya yi da za mu yi bankwana.”

Ƙungiyar Manchester City ta ce za ta shirya wani bikin bankwana na musamman domin girmama ɗan wasan kafin kakar ta ƙare.

De Bruyne ya koma City daga Wolfsburg a kan fan miliyan 55, kuma ya taimaka sosai wajen nasarorin da ƙungiyar ta samu, ciki har da lashe kofin Zakarun Turai karo na farko a tarihinta, inda suka doke Inter Milan a wasan ƙarshe a birnin Istanbul.

Sai dai ɗan wasan ya sha fama da rauni a ‘yan shekarun nan, inda ya shafe watanni biyar yana jinya a kakar da ta wuce.

A kakar bana, ya buga wasanni 26 kacal a dukkanin gasa.

De Bruyne, ya fara wasan ƙwallon kafa a kulob din Genk na Belgium, kafin Chelsea ta saye shi a watan Janairu 2012 a kan fan miliyan bakwai.

Ya buga wa Chelsea wasanni tara kacal sannan aka tura shi aro zuwa Werder Bremen, daga nan ya koma Wolfsburg a 2013, kafin komawarsa City.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barin Kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tube a cikin daki

An tsinci gawar wani matashi da budurwarsa a tube bisa gado a cikin dakinsa a yakin Alo da ke Karamar Hukumar Ankpa a Jihar Kogi.

An tsinci gawara masoyan ne a gidan hayan da saurayin ke zama ranar Juma’a da ta gabata.

Mai gidan hayan mai suna Salisu Ibrahim ne ya nemi agajin jama’a sakamakon rashin ganin matashin ya bude kofarsa da safe kamar yadda ya saba.

Daga nan ne ya sanar da dan uwan matashin da kuma ’yan sanda, inda suka so aka balla kofar dakin, inda aka samu masoyan sun kwanta dama.

Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72 HOTUNA: An yi zanga-zangar adawa da matsalar tsaro a Filato NAJERIYA A YAU: Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Tsarin Mulkin Najeriya?

Ya ce da shigan dan uwan mamamcin ya tsinci gawar masoyan biyu tsirara a bisa gado bayan da aka balla kofar dakin.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin ’yan sandan jihar Kogi, SP William Aya, ya ce suna gudanar da bincike domin gano hakikanin abin da ya faru.

Aya ya ce, ”DPO na Ankpa na ya tura jami’an da suka je aka gano gawarwakin aka kai su asbiti a Ankpa inda aka tabbatar rai ya yi halinsa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe
  • Dalilin Da Zai Iya Hana Ni Sake Bugawa Manchester United Wasa – Rashford
  • Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
  • Majalisun jihohi sun buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Makiyayi Da Dabbobi 4 A Wani Hari A Filato
  • Kotu A Kano Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wani Matashi Da Ya Kashe Ƙanwarsa Da Kishiyar Mahaifiyarsa
  • Manchester United Na Zawarcin Matheus Cunha Na Wolves
  • Hargitsi A Filin Wasan Kwallon Kafa Tsakanin Al-Ahly Tripoli Da Al-Suwaihli A Kasar Libiya
  • An tsinci gawar saurayi da buduwarsa a tube a cikin daki