Aminiya:
2025-05-14@17:16:07 GMT

’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili

Published: 4th, April 2025 GMT

Tsohon Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Kano kuma tsohon Mashawarci na Musamman ga Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, CP Muhammad Wakili (ritaya), ya jaddada cewa dole ne ’yan sanda su yi amfani da ikon da suke da shi cikin gaskiya da adalci, don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Da yake jawabi a wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Gombe, a matsayin wani ɓangare na bikin makon ’yan sanda, CP Wakili ya ce ba zai yiwu jami’an tsaro su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata ba tare da goyon bayan al’umma ba.

An ceto yara ’yan Taraba da aka yi safararsu zuwa Kudu Adadin waɗanda suka mutu a harin Filato ya kai 52

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su kasance ƙofar su a buɗe ga jama’a, su saurari ƙorafe-ƙorafensu, tare da gina kyakkyawar alaƙa da su.

” ’Yan sanda ba abokan gaba ba ne ga jama’a, su ne ginshiƙin tsaro da ci gaba. Amma dole ne su kula da yadda suke amfani da ikon da aka ba su, domin kada ya rikiɗe ya zama cin zarafi,” in ji Wakili.

Ya yabawa Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, bisa ƙwazon da yake nunawa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Wakili ya kuma buƙaci al’umma da su bada haɗin kai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Gombe da ƙasa baki ɗaya.

A nasa jawabin, Kwamishinan ‘Yan sanda na Gombe, CP Bello Yahaya, ya jaddada cewa Ranar ‘Yan Sanda ta Duniya, da ake gudanarwa duk shekara na da nufin tunawa da irin rawar da ’yan sanda ke takawa wajen tabbatar da tsaro.

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su ƙara ƙaimi wajen kusantar da kansu ga jama’a, su nuna gaskiya da ƙwarewa a ayyukansu, domin gina amana da fahimtar juna.

A nasa ɓangaren, Kwamishinan Harkokin Tsaro da Cikin Gida na Gombe, Laftanar Kanar Abdullahi Bello (ritaya), ya jinjinawa CP Yahaya bisa shirya wannan muhimmin taro.

“Wannan irin shiri yana taimakawa wajen gina kyakkyawar fahimta tsakanin jami’an tsaro da jama’a. Ina kira ga rundunar ’yan sanda da su ci gaba da irin waɗannan shirye-shirye,” in ji shi.

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa manufar wannan bikin ita ce kusantar da jama’a ga ’yan sanda tare da inganta ayyukansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda CP Muhammad Wakili Gwamna Inuwa Yahaya

এছাড়াও পড়ুন:

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

A cikin binciken jin ra’ayoyin, kashi 91 cikin 100 na masu bayyana ra’ayoyi, sun yi imanin cewa shaye-shayen miyagun kwayoyi na daga cikin manyan abubuwan da ke barazana ga rayuwar Amurkawa.

An wallafa sakamakon binciken a dandalolin CGTN a cikin harsuna biyar da suka hada da Ingilishi, Sifaniyanci, Faransanci, Larabci, da Rashanci. A tsakanin sa’o’i 24 da kaddamar da binciken, masu amfani da intanet fiye da 12,000 ne suka shiga cikin binciken tare da bayyana ra’ayoyinsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe
  • Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi
  • Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
  • Iran ta yi tir da sabbin takunkumin ‘rashin adalci’ da Amurka ta kakaba mata
  • Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano
  • Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
  • Ƴan Ta’adda Sun Yi Garkuwa Da Tsohon Jami’in Shige Da Fice Da Fasinjoji 2 A Yobe
  • Jami’ar Maryam Abacha ta rufe ɗakunan kwanan ɗalibai a Kano
  • Mahara sanye da kayan ’yan sanda sun kashe malami sun sace mata 3 a makaranta a Zamfara
  • NAJERIYA A YAU: Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Na GMO