HausaTv:
2025-04-25@08:11:55 GMT

 Falasdinawa 86 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata

Published: 4th, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu ta sanar da cewa adadin wadanda su ka yi shahada a cikin sa’o’I 24 da su ka wuce, sun kai 86, yayin da wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 287.

Asibitocin yankin na Gaza sun karbi wannan adadin na  shahidai da kuma wadanda su ka jikkata, suna karbar magani.

Ma’aikatar harkokin kiwon lafiyar ta Falasdinawa ta kara da cewa ya zuwa yanzu jumillar Falasdinawan da HKI ta kashe tun daga 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu sun haura dubu 50.

Bugu da kari a halin da ake ciki da akwai gawawwakin shahidai masu yawa da suke kwance a karkashin baraguzan gidajen da HKI ta rushe da mutane a cikinsu, da kuma wadanda ta kashe akan hanya a lokacin da suke tafiyar zuwa inda za su sami mafaka.

Yankunan da HKI ta tsananta kai wa hare-hare a yau sun hada Khan-Yunus da kuma Arewacin Rafah.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu

Majiyar fadar Vatican ta bada sanarwan cewa za’a gudanar da jana’izar paparuma Francis a ranar Asabar mai zuwa 26 ga watan Afrilu a dandalin st. Peter dake birnin Vatican amma za’a ajiye gawarsa don yi mata kallo na karshe a daga gobe Laraba a St. Peter’s Basilica har zuwa ranar Jana’izar.

Shafin yanar gizo na labarai “Africa News” ya bayyana cewa paparoma Francis ya mutane a ranar 20 ga watan Afrilu yana dan shekara 88 a duniya, kuma fatansa a cikin jama’a da kuma jawabinda na karshe kwana guda ne kafin rasuwarsa.

Labarin ya kara da cewa paparoman ya shahara da son talaka, da kuma wadanda aka zalunta, musamman al-ummar Falasdinu, wadanda yahudawan HKI suke yiwa kissan Gila tun sdhekara ta 2023.

Cardinal-cardinal na catholica sun fara taro a Vatican a yau Talata don neman wanda zai gajesi a cikinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta
  • Jirgin Farko Daga Minna Zuwa Abuja Ya Nuna Haɗin Gwiwar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi – Minista
  • Ƙasurgumin Ɗan Fashin Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Mutu Bayan Arangama Da ‘Yansanda A Kano
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 112
  • Yawan Falasdinawan Da Suka Yi Shahada Sakamakon Hare-Haren ‘Yan Sahayoniyya Sun Kai 51,266
  • Za’a Yi Zana’izar Paparoma Francis A Ranar Asabar 26 Ga Watan Afrilu
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Goyon Baya Daga Sauran Falasdinawa Na Gabar Yammacin Kogin Jordan