HausaTv:
2025-04-25@06:00:05 GMT

Sayyid Husi: Hare-haren Amurka Ba Za Su Yi Tasiri Akan Karfinmu Ba

Published: 4th, April 2025 GMT

Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdulmalik al-Husi ya bayyana cewa; Al’ummar musulmi suna fuskantar manyan hatsari guda biyu,  da su ka hada laifukan da HKI take tafkawa a Gaza, da kuma kokarin shafe hakkokin falasdinawa baki daya.

Shugaban kungiyar ta Ansarullah ya kuma tabo batun keta tsagaita wutar yaki da HKI take yi a kasar Lebanon yana mai kara da cewa, keta hurumin kasar Lebanon da ‘yan sahayoniyar suke yi, ya isa har birnin Beirut.

Akan kasar Syria ma, jagoran na kungiyar Ansarullah na Yemen ya yi ishara da hare-haren da ‘yan sahayoniya su ka kai  a cikin biranen Damascus, Hums da Dar’a.

Sayyid Abdulmalik al-Husi ya ce,abokan gaba sun mayar da keta hurumin kasashen al’umma abinda za su rika yi kodayaushe. Haka nan kuma ya ce ko kadan bai kamata a mayar da kisan da ake yi wa Falasdinawa ya zama wani abu da ake gani yana faruwa a kowace rana ba.

Sayyid Abdulmalik ya yi kira da a sake dawo da fafutukar da ake yi a duniya baki daya, ta nuna kin amincewa da abinda yake faruwa a Gaza ba.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka

Sai dai a hakika, ba dole ne kasar Lesotho, da sauran kasashen Afirka su mika wuya ga kasar Amurka, don ta ci zalinsu yadda ta ga dama ba. Kamar yadda Charles Olunaiju, wani masanin kasar Najeriya, ya rubuta a cikin wata makalarsa da jaridar Vanguard ta wallafa, kasar Amurka ba za ta samu biyan bukata a yakin ciniki da ta tayar ba, saboda dunkulewar duniya sakamakon dimbin cinikin da ake yi tsakanin kasashe daban daban, da hadewar sassan duniya da cudanyar mabambantan al’adu, wadanda aka samu bisa tushen ci gaban fasahohi, sun haifar da wani yanayi mai armashi da ba za a iya sauya shi ba.

 

Mista Olunaiju ya kara da cewa, a matsayin wata dabarar tinkarar rikici, kasashen Afirka za su iya amfani da tsarin yankin ciniki mai ‘yanci na nahiyar Afirka (AfCFTA) wajen mai da nahiyar dunkulallun kasuwanni, da babban yankin da ake zuba masa jari, ta yadda za a ba kasashen Afirka damar aiwatar da Ajandar Raya Kasa ta 2063 yadda ake bukata. A sa’i daya kuma, kasar Sin, bisa matsayinta na abokiyar hulda mafi muhimmanci a fannin cinikayya ga kasashen Afirka, za ta samar da taimako ga nahiyar Afirka a kokarinsu na tabbatar da zaman lafiya, da walwala, in ji Mista Olunaiju.

 

Sa’an nan, a nasa bangare, Dennis Mwaniki, shahararren mai nazarin manufofin hukumomi dan kasar Kenya, yana da ra’ayin iri daya dangane da yakin cinikin da kasar Amurka ta kaddamar, inda ya ce, matsin lamba da Amurka ta dora wa kasashen Afirka zai sa su kara karkata ga kasar Sin, da sauran manyan tattalin arziki dake tasowa. Saboda yayin da kasar Amurka ke rufe kofarta, sauran kasashe sun ba da karin damammakin kulla huldar ciniki, wadda za ta samar da sakamako mai gamsarwa. Sabanin matakin kasar Amurka na karbar karin harajin kwastam, kasar Sin ta yafe wa kasashe masu raunin tattalin arziki harajin kwastam, da ba su sauran tallafi da gatanci, lamarin da ya janyo hankalin dimbin ‘yan kasuwan kasashen Afirka ga kasuwannin kasar Sin mai yawan al’umma da ya kai biliyan 1.4. Mista Mwaniki ya jaddada cewa, “Wannan tsari zai tabbatar da moriyar kowa, ba kamar manufar da Donald Trump ya daukaka ta Cin Moriya daga Faduwar Wani ba.”

 

Ban da haka, jawabin da jakadan kasar Sin a Najeriya Yu Dunhai ya yi, a birnin Abuja a kwanan baya, ya zama mai goyon bayan maganganun da masanan kasashen Afirka suka fada, inda jakadan ya ce, ya kamata a kalli yakin ciniki a matsayin wata damar karfafa huldar hadin kai tsakanin kasashen Sin da Najeriya, gami da tsakanin Sin da kasashen Afirka baki daya. Yanzu kasashen Afirka na kokarin farfado da tattalin arzikinsu, saboda haka suna bukatar tsarin ciniki mai ‘yanci da ya shafi bangarori daban daban, da wani muhallin kasuwanci da ake iya hasashen yanayinsa na nan gaba. Yayin da kasar Sin a nata bangare take dukufa wajen bude kofarta ga kasashen ketare, da kokarin taimakon kasashen Afirka wajen raya kansu a kai a kai, matakan da ke da muhimmanci ga yunkurin saukaka yanayin rashin tabbas da ake fuskantar sakamakon yakin ciniki.

 

Sai dai wadanne matakai ne za a iya dauka don tinkarar yakin ciniki? Za mu iya ci gaba da daukar misalin kasar Lesotho, inda kayayyakin da take fitarwa kasar Amurka, idan Amurka ba ta so, to, za a iya bin shawarar Madam Ngozi Iweala, wadda ta ce sai a sayar da su ga sauran kasashen dake nahiyar Afirka. Ban da haka, kasar Lesotho za ta iya hadin gwiwa da kasar Sin wajen inganta tsarin masana’antu, ta yadda za ta lalubo sabuwar damar ciniki. Ganin yadda kasar Sin ta zama kasa ta farko da ta kulla huldar hadin kai bisa manyan tsare-tsare tare da Lesotho, kana adadin cinikin da ake yi tsakanin kasashen 2 ya riga ya karu zuwa dala miliyan 150 a bara.

 

Sinawa kan ce, “Dabara ta fi matsala yawa.” Mu yi kokarin tinkarar kalubale, ta yadda za a iya mayar da shi damar raya kai. (Bello Wang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora: Tafarkin Imaman Ahlul Bayti ( A.S) Na Gwgawarmaya Ne Da Jajurcewa
  • Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Ba ‘Yan Nijeriya Ne Ke Kai Mana Hare-hare A Benuwai Ba – Gwamna Alia
  • Yawan Falasdinawan Da Suka Yi Shahada Sakamakon Hare-Haren ‘Yan Sahayoniyya Sun Kai 51,266
  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar
  • Hezbollah, ta yi tir da Isra’ila kan kisan gillar da aka wani babban jigonta
  • Kungiyar BRICK Ta Rattaba Hannu A Kan Yarjeniyar Raya Ayyukan Noma A Duniya
  • Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka
  • Ganduje Ya Soki Buba Galadima, Ya Ce “Ɗan Siyasa Ne Mara Tasiri”