Aminiya:
2025-04-25@07:59:27 GMT

An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai

Published: 5th, April 2025 GMT

Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja, a ranar Juma’a, ta haramta wa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio tattaunawa da manema labarai yayin da ’yar majalisar ta shigar da ƙara a gaban kotu.

Mai shari’a Binta Nyako ce ta yanke hukuncin a ranar Juma’a bayan ƙorafin da lauyan da ke kare Akpabio ya yi cewa Natasha na bin daga wannan gidan talabijin zuwa wancan, don tattaunawa da manema labarai kan shari’arsu, duk da cewa batun yana gaban kotu.

’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili An ceto yara ’yan Taraba da aka yi safararsu zuwa Kudu

Kotun ta ce daga yanzu babu wani ɓangaren da zai tattauna da manema labarai dangane da batun.

“Bai kamata a yi hira da manema labarai daga kowane ɓangare da lauyoyi dangane da batun wannan lamari ba, babu batun yaɗa labarai kai tsaye ko yaɗa labarai kan lamarin.

“Bai kamata a yi hira da gidan talabiji ba game da wannan batu. Kamata ya yi a toshe kafafen yaɗa labarai baki ɗaya,” in ji mai shari’a Nyako.

A ranar Alhamis ne babban alƙalin kotun, Mai shari’a John Tsoho, ya mayar da shari’ar ga mai shari’a Nyako.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: da manema labarai

এছাড়াও পড়ুন:

Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji

Babban Hafsan Sojin Ƙasa na Najeriya, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede, ya ba wa dakarun rundunar wa’adin wata guda su fatattaki sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta Mahmud a da ta ɓulla a Jihar Kwara.

Oluyede ya ba da wannan umarnin ne a lokacin da yake jawabi ga sojojin a ziyarar da ya kai Barikin Sobi da ke Ilorin, babban birnin jihar.

“Daga wata mai zuwa, ba na son in ƙara jin mostin waɗannan ’yan ta’addan a yankin Dam ɗin Kainji,” in ji babban hafsan sojin.

Ya umarce su da su kawar da ’yan ta’addan daga ƙananan hukumomi biyun da suka addaba, yana mai jaddada cewa yana son a kammala aikin cikin wata mai zuwa.

Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa gidan rediyo na haɗin gwiwa NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci

Babban hafsan sojin ya ce Najeriya ba za ta iya ba da damar ’yan fashin daji ko ’yan ta’adda su ƙara yaɗuwa zuwa wani ɓangare na ƙasar ba.

“Don haka, kuna nan kuma na san za ku yi hakan don tabbatar da cewa waɗancan mutanen sun bar mana wannan wurin,” kamar yadda ya shaida wa sojojin.

“Idan suna son shiga wata ƙasa, wannan su ta shafa, amma dole ne ku kawar da su daga waɗannan dazuzzukan don kada mu sake samun wata ƙungiyar Boko Haram da za ta dame mu a nan.

“Ina iya gaya muku, cikin wata mai zuwa, al’amura za su bambanta. Abin da ke faruwa a Kwara ba zai iya yin barazana ga zaman lafiyar Najeriya gaba ɗaya ba; lamari ne keɓantacce kuma za mu magance shi kai tsaye.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • ICC ta ki amincewa da bukatar Isra’ila na soke sammacin kama Netanyahu
  • Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam
  • Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji
  •  Ghana Ta Fada Cikin Takaddama Bayan Tisge Babbar Mai Shari’a Ta Kasar Da Shugaban Kasa Ya Yi
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso
  • Iran Ba Ta Da Niyyar Tattaunawa Da Amurka A Fili Bainar Jama’a Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Iran Ta Jaddada Matsayinta Kan Batun Tace Sinadarin Yuranium A Batun Tattaunawa Da Amurka