Wani Kusa A Kungiyar Hamas Ya Yi Shahada A Wani Harin Isra’ila A Kudancin Lebanon
Published: 5th, April 2025 GMT
An kashe wani kusa a kungiyar Hamas Hassan Farhat, wanda aka fi sani da Abu Yasser, da wasu mutane biyu a wani hari da jiragen yakin Isra’ila suka kai a wani gida a birnin Sidon, dake kudancin kasar Lebanon, a safiyar jiya Juma’a.
A cewar Al-Mayadeen, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai wani hari ta sama kan wani gida da ke birnin Sidon da ke kudancin kasar Lebanon, inda harin ya kashe babban kusa na Hamas Hassan Farhat da wasu mutane biyu daga cikin iyalansa.
A cewar rahoton, sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun kai hari a Al-Naqoura, Nabatiyeh, da Sidon a kudancin kasar Lebanon a yammacin ranar Alhamis, inda suka yi barna a yankunan da aka kai harin.
Shafin tashar “Russia Today” ya bayar da labarin cewa: Bisa kididdigar farko da aka yi, “Hassan Farhat, wanda aka fi sani da Abu Yasser”, shugaban kusa a kungiyar Hamas, da dansa da ‘yarsa ne suka yi shahada a wani hari da jiragen Isra’ila suka kai a wani gida a yankin Dala’a a tsakiyar garin na Sidon. A wannan harin da aka kai ta hanyar amfani da jirgi maras matuki, an harba makamai masu linzami guda biyu a gidan.
Kawo yanzu kungiyar Hamas ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance game da shahadar Farhat ba, inda ta jaddada matsayinta na ci gaba da bin tafarkin neman ‘yanci wanda Farhat da iyalansa suka yi shahada a kansa.
Dangane da haka ne ma’aikatar lafiya ta kasar Labanon ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa akalla mutane uku ne suka rasa rayukansu wasu biyu kuma suka jikkata sakamakon wannan hari da jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai a birnin da ke kudancin kasar Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kudancin kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
Wani mummunan al’amari ya girgiza al’umma a Ƙaramar Hukumar Kwami, Jihar Gombe, inda ake zargin wani magidanci ya jagoranci sacewa da kashe ɗansa mai shekara shida domin yin tsafin kuɗi.
Ana zargin cewa mahaifin yaron shi ne jagoran kisan kuma Yana cikin waɗanda suka tsere, a yayin da hukumomi ke ci gaba da farautar sa.
Tuni ’yan sanda suka cafke mutane takwas bisa zargin wannan aika-aika a unguwar Bura-Bunga da ke ƙaramar hukumar.
Kakakin ’yan sanda a Jihar Gombe, DSP Buhari Abdullahi, ya sanar cewa waɗanda suka shiga hannu sun amsa cewa sun kashe yaron ne bisa umarnin bokaye da suka nemi sassan jikin ɗan Adam don yin tsafin kuɗi.
An kama mutane 13 kan zubar da ciki a Bauchi ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a NasarawaBincike ya nuna wani mai shekaru 45, wanda ake zargin shi ne shugaban gungun, ya hallaka yaron tare da raba sassan jikinsa gida biyu.
Ɓangaren sama na jikinsa an jefa shi cikin rijiyar, yayin da ɓangaren kasa aka bai wa abokan laifinsa.
Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu bokaye biyu ne suka nemi sassan jikin yaron, kuma wani matashi mai shekaru 18 ne ya sace yaron, sannan wani ya haɗa bokayen da su.
Kwamishinan ’yan sanda, CP Bello Yahaya, ya bayyana cewa za a tabbatar an gurfanar da duk masu hannu a wannan mummunan kisa a gaban ƙuliya.
Ya kuma yi kira ga jama’a su riƙa sa ido tare da bayar da rahoto kan duk wani abu mai kama da waɗanda ake nema jami’an tsaro.
Rundunar ’yan sanda ta jaddada aniyarta na kawo ƙarshen irin waɗannan munanan laifuka a faɗin jihar ta Gombe.