Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu
Published: 5th, April 2025 GMT
Dubun-dubatar al’ummar kasar Aljeriya sun gudanar da wani gagarumin gangami da jerin a wannan Juma’a a birnin Algiers babban birnin kasar, domin yin Allawadai da laifukan yaki da Haramtacciyar Kasar Isra’ila take aikatawa a kan al’ummar yankin zirin Gaza.
Kamar yadda kungiyar Movement of Society for Peace ta yi kira, dubban ‘yan kasar Aljeriya ne suka fito domin nuna goyon baya ga al’ummar Palasdinu a gaban hedikwatar jam’iyyar da ke unguwar al-Mouradia, babban birnin kasar Aljeriya.
Sai dai hukumomin Aljeriya sun kewaye masu zanga-zangar don hana fadada zanga-zangar zuwa wuraren da jama’a ke taruwa.
Masu zanga-zangar sun yi ta rera taken nuna rashin amincewarsu da kisan kiyashin da “Isra’ila” ke yi a Gaza, inda suka yi Allah wadai da saka al’ummar Gaza a cikin yunwa da kuma ci gaba da aiwatar da kashe-kashen da Isra’ila ke yi, da nufin tilasta wa al’ummar Palasdinu kauracewa gidajensu da yankunansu . Masu zanga-zangar sun kuma yi kira da a rufe ofishin jakadancin Amurka da ke Aljeriya, saboda rawar da Amurka ta take takawa wajen mara wa Isra’ila baya ga laifukan Isra’ila a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
Mutane 47 ne suka rasa rayukansu tare da jikkatan wasu da dama a harin da aka kai da jirgin sama kan birnin El-Fasher na kasar Sudan
Runduna ta 6 da ke yankin El- Fasher ta sanar da mutuwar fararen hula 47 tare da jikkata wasu da dama sakamakon kazamin lugudan wuta da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka yi kan birnin El- Fasher, fadar mulkin jihar Darfur ta Arewa.
A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ta ce: Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Rapid Support Forces na ci gaba da kai hare-hare kan fararen hula, inda suka yi amfani da harsasai masu yawa a yayin da suka yi ruwan wuta a kan unguwannin birnin El-Fasher a wannan mako, inda suka kashe fararen hula 47, ciki har da mata 10, wadanda hudu daga cikinsu sun kone a cikin gidajensu. Sannan an kashe mata hudu a wani bangare, yayin da mata biyu an kashe sune a lokacin da suke tafiya.