Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin Kano
Published: 5th, April 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Kano, ta bayyana cewa ɗaliban makarantun kwana na gwamnati da na masu zaman kansu za su koma makaranta a ranar Lahadi 6 ga watan Afrilu, 2025.
Wannan ya shafi makarantun firamare da sakandare domin ci gaba da zangon karatu na uku na shekarar 2024 zuwa 2025.
Boko Haram haram ta kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labaraiGa ɗaliban makarantun jeka ka dawo kuwa, za su koma makaranta a ranar Litinin 7 ga wata.
Sanarwar da Daraktan Wayar da Kai na Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru, ya fitar, ta buƙaci iyaye da su kula da wannan rana domin tabbatar da cewa yara sun koma makaranta a kan lokaci.
Kwamishinan Ilimi na Jihar Kano, Dokta Ali Haruna Makoda, ya gargadi ɗalibai da su guji kawo miyagun abubuwa kamar wuƙa, reza ko ƙwayoyi zuwa makaranta.
Ya kuma ce gwamnati za ta ɗauki mataki a kan duk ɗalibin da ya ƙi bin wannan doka.
Ya ƙara da cewa bin doka da ƙa’ida na taimaka wa ɗalibai su samu nasara a karatunsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibai gwamnati Komawa Makaranta Ma aikatar ilimi koma makaranta
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB
Ya buƙaci jama’a da su ci gaba da tallafa wa jami’an tsafta domin tabbatar da tsaftar muhalli a jihar.
Aikin tsaftar muhalli na wata-wata, wanda ake yi a ƙarshen kowane wata, ana dakatar da zirga-zirgar ababen hawa na wasu awanni domin tsaftace muhalli a faɗin Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp