Adadin mutanen da suka mutu a girgizar kasa a Myanmar ya karu zuwa 3,354
Published: 5th, April 2025 GMT
A Myanmar adadin mutanen da suka mutu a girgizar kasar ya karu zuwa 3,354 a gwamnatin mulkin sojan kasar.
Girgizar kasar ta kuma jikkata wasu mutane 4,850, sannan akwai wadanda har yanzu kuma ba a gansu ba.
Bayanai sun ce bala’in na iya kara kawo cikas ga gwamnatin mulkin sojan kasar.
Myanmar dai na cikin rudani bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a shekarar 2021.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Arakci: Mun Yi Tattaunawa Mai Kyau Da Mahukuntan Kasar China
Ministan harkokin wajen Iran wanda ya ziyarci kasar China, ya bayyana cewa, tattaunawa da mahukunta wannan kasa ta yi kyau, kuma ba da jimawa ba, shugaban kasar Iran zai kai Ziyara can kasar.
Ministan harkokin wajen na Iran Abbas Arakci bayan ganawa da takwaransa na China ya ce; Na yi doguwar ganawa da ministan harkokin wajen China, wacce take mai muhimmanci, kuma kusan dukkanin bangarorin da suka shafi alakar tsakanin kasashenmu biyu mu ka tattauna, haka nan kuma batutuwa da su ka shafi siyasar kasa da kasa.”
Arakci ya kara da cewa; Da akwai fahimtar juna a tsakaninmu, musamman abinda ya shafi batun makamashin Nukiliyar Iran na zaman lafiya, da tataunawar da ake yi da Amurka.”
Haka nan kuma ya bayyana wasu daga cikin abubuwan da su ka tattauna da su ka hada siyasar Amurka da halayyarta ta nuna karfi, da kokarin da take yi na mamaye fagen siyasar kasa da kasa.
Ministan harkokin wajen na Iran ya kuma yi Magana akan ziyarar da shugaban kasar Iran zai kai zuwa kasar China wacce za ta kasance ba da jimawa sosai ba.