Al-Houthi: Hare-haren Amurka sun kasa dakatar da gwagwarmayar Yeman
Published: 5th, April 2025 GMT
Madugun kungiyar Ansarallah ta kasar Yeman ya yi ikirarin cewa, zafafan hare-haren wuce gona da iri da Amurka ke kaiwa kasar Yemen, ya kasa dakatar da ayyukan gwagwarmayar Yeman na goyon bayan al’ummar Gaza ko kuma kare jiragen Isra’ila a tekun Bahar Rum.
A wani jawabi da ya yi a ranar Juma’a, Abdul-Malik al-Houthi ya ce Amurka ta zafafa kai hare-hare a kan kasar Yemen, inda wasu lokutan ta kai hare-hare sama da 90 a kowace rana, a wani bangare na goyon bayan da take baiwa kasar Isra’ila a yakin kisan kare dangin da ta ke yi a zirin Gaza.
Duk da haka, ya jaddada cewa, hare-haren na Amurka “sun kasa dakatar da ayyukan soji da ke tallafawa al’ummar Falasdinu, ko kuma tabbatar da kare zirga-zirgar jiragen ruwa na Isra’ila a cikin Bahar Maliya, Gulf na Aden da kuma Tekun Oman.”
Ya kuma ce jami’an sojin Amurka sun amince cewa hare-haren sun kasa dakile karfin sojojin Yemen.
Al-Houthi ya ce: “Amurka ta gaza cimma burin da ta sanya a gaba na kawar da shugabanni da kuma kawar da ‘yantacciyar kasar Yemen.”
Ya yi alkawarin cewa kasar Yemen za ta ci gaba da kai hare-hare na daukar fansa, kafin ya bayyana cewa: “Amurka ba ta tsoratar da mu.”
Shugaban kungiyar Ansarallah ya kuma gargadi gwamnatocin kasashen Larabawa da kasashen da ke makwabtaka da su kan goyon bayan hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen sannan ya kara da cewa kutsawar da Ministan Isra’ila mai tsatsauran ra’ayi, Itamar Ben-Gvir ya yi a harabar masallacin Kudus, shaida ce ta ci gaba da cin zarafi da Isra’ila ke yi kan “daya daga cikin mafi girman wurare masu tsarki ga musulmi.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ta bayyana cewa; Kakaba takunkumi kan kasarta ya sabawa ikirarin Amurka na yin shawarwari da ita
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan matakin da Amurka ta dauka na kakabawa wasu gungun mutane masu alaka da bangaren makamashi, man fetur da iskar gas da kuma wasu mutane da dama masu fafutuka a shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran na lumana takunkumi.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, Baqa’i ya bayyana manufar takunkuman da Amurka ta kakabawa al’ummar Iran da cewa; A fili take nuna kyama ga masu yanke shawaran Amurka kan al’ummar Iran da kuma nuna rashin mutunta doka da hakkin dan Adam ne.
Ya kara da cewa: Dogaro da tsarin gwamnatocin Amurka da suka shude kan takunkumin tattalin arziki a kan kasashe masu tasowa, a matsayin makamin tsoratarwa da matsin lamba na siyasa, wani lamari ne da ya saba wa muhimman ka’idojin Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma dokokin kasa da kasa, kuma yana yin zagon kasa ga ginshikin doka da ka’idojin ciniki cikin ‘yanci, kuma yana haifar da keta hakkin bil’adama na asali na al’ummomin da takunkumin ya shafa, musamman ‘yancin ci gaba. Wannan hali sau da yawa yana zama laifi ga ɗan adam.