Aminiya:
2025-04-27@03:56:29 GMT

Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang

Published: 5th, April 2025 GMT

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang ya ce hare-hare da kashe-kashen da ake yi a wasu sassan jihar wasu ne ke ɗaukar nauyinsu ba rikicin manoma da makiyaya ba ne.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin bikin baje kolin kayayyaki da fasaha da ƙungiyar Tincity Fashion Week ta shirya a daren Juma’a a Abuja.

An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe Sabon harajin Trump zai jefa tattalin arziƙin duniya cikin matsala — WTO

Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya NAN ya bayar da rahoton cewa, a ranar 2 ga watan Afrilu, wasu ’yan bindiga sun kai hari a ƙauyukan Manguno, Daffo da Josho na ƙaramar hukumar Bokkos  ta jihar.

Maharan sun kashe mutane da dama tare da lalata gidaje da wasu kadarori na miliyoyi.

Mutfwang, wanda ya jaddada cewa hare-haren an tsara shi ne, ya yi alƙawarin cewa gwamnati da hukumomin tsaro sun tanadi matakan daƙile afkuwar lamarin nan gaba.

“Ina so in gode muku da kuke nan domin goyon bayanku da kuma karrama Filato tare da halartarku a wannan taron, ba mu ɗauki wannan haɗin kai da wasa ba.

“Mun yi tunanin dakatar da wannan taron ne saboda yanayin tsaro da jihar ke fama da shi, amma mun yanke shawarar kada lamarin ya lalata mana kyawawan abubuwan da ya kamata mu yi na taron biki.

“Kuma dole ne in ce manufar maƙiya ita ce jefa jihar cikin ruɗu da baƙin ciki, amma za mu kauda  manufarsu ba za mu ba damar yin abin da suke so ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Caleb Mutfwang

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen

Jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-haren a kan biranen San,a,Sa’adah da kuma Hudaidah na kasar Yemen.

Kamfanin dillancin labarun “Saba’a” na kasar Yemen ya nakalto cewa sojojin na Amurka sun kai hare-hare har sau uku a dutsen Naqam, wanda  yake gabashin birnin San’aa.

Kamfanin dillancin labarun na “Saba’a” ya kuma ce, jiragen yakin Amurka din sun kai hare-haren ne a tsakanin marecen jiya Laraba da kuma safiyar yau Alhamis.

Daga cikin wuraren da aka kai wa harin jiya da marecen da akwai Sahlin dake karamar hukumar Ali-Salim. Sau 6 Amurkan ta kai wa yankin hare-hare.

Da safiyar yau Alhamis kuwa jiragen yakin na Amurka sun kai hare-hare a gundumar Sa’adah.

Wasu yankunan da su ka fuskanci hare-haren su ne, al-tahita, dake kudancin gundumar Haudaidah, a yammacin kasar ta Yemen.

Amurka tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda  bayar da kariya ga HKI, da zummar hana Yemen kai hare-hare akan manufofin ‘yan sahayoniya a ruwan tekun ” Red Sea”.

Kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ta bayyana cewa ba za ta taba daina kai wa HKI hare-haren ba har sai idan an daina kai wa Gaza hari. Bugu da kari ta sanar da cewa;za ta ci gaba da hana jiragen ruwa wucewa ta tekun “Red Sea” har zuwa lokacin da za a kawo karshen hana shigar da kayan agaji cikin yankin na Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Gwamnatin Kano Ta Gano  An Biya Wasu Ma’aikatan Bogi Naira Miliyoyi
  • Rashin Wutar Lantarki: Jihohin Kano, Katsina Da Jigawa Na Samun Wutar Awa 2 Ne Kacal A Kullum
  • Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4
  • Tinubu Ya Tabbatar Da Aniyar Gwamnatinsa Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro
  • Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen
  • Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni
  • Gwamnatin Kano Da NBC Sun Shirya Taron Bita Domin Tsaftace Harkar Siyasa
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Iran za ta karbi bakuncin taron farko kan kare hakkin dan Adam a Gabas ta tsakiya