Babban kocin Super Eagles, Eric Chelle, ya amince cewa zai yi wuya a shawo kan matashin dan wasan gaban Arsenal Ethan Nwaneri ya buga wa Nijeriya wasa, an haifi Nwaneri a Kasar Ingila amma kuma mahaifinshi dan Nijeriya ne yayin da mahaifiyarsa ta ke ‘yar Ingila.

Dan wasan mai shekaru 18 ya riga ya bugawa Ingila wasa amma har yanzu yana iya sauya sheka zuwa Nijeriya, Chelle ya yi ikirarin cewa kocin tawagar Ingila da ake wa lakabi da Three Lions, Thomas Tuchel, shi ma ya na sha’awar ya yi amfani da dan wasan mai buga gaba a matakin kasa.

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Legas, Mutane 10 Sun Kamu CMG Ya Nuna Fina-Finan “Documentary” Bisa Jigon “Kama Hanyar Samar Da Wadata”

Chelle ya shaida wa SCORENigeria cewa “A lokacin tafiyata zuwa Ingila (don ganawa da taurarin Nijeriya irin su Aled Iwobi da Wilfred Ndidi), na ce zan so Nwaneri ya buga wa Nijeriya wasa.”

“Saboda haka ina fatan hukumar kwallon kafa ta Nijeriya (NFF) za ta yi magana da shi, sannan ni ma zan yi magana da shi, domin shawo kansa zai yi wahala saboda Ingila ma za ta so ta mayar da shi cikakken dan wasanta dake buga wasannin kasa da kasa, amma na yi imanin zan iya gamsar da shi saboda zan yi magana da shi game da yanayin wasan da kuma abin da ya dace bayan NFF ta tuntuve shi”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan

‘Yan gudun hijira a Sudan sun yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su ceto yara da tsofaffi daga mummunan kangin da suka shiga

An gwabza kazamin fada a kusa da birnin El Fasher da ke arewacin Darfur tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, wadanda suka yi ruwan bama-bamai kan birnin da na manyan bindigogi, inda suka kashe fararen hula akalla 35.

Sojojin Sudan sun samu nasarar dakile wadansu daga cikin wadannan hare-hare, amma duk da haka sun janyo hasarar rayukan bil’adama da na dukiya. Sannan  sojojin Sundan sun kuma kwace iko da birnin Bara da ke Arewacin Kordofan, kofar Nyala a Kudancin Darfur.

Dakarun kai daukin gaggawa sun yi wa birnin kawanya da nakiyoyi da ramuka da nufin yiwuwar harin farmakin sojojin Sudan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Sun Yi Kira Ga Kungiyoyin Kasa Da Kasa Da Su Ceto Yara Da Tsofaffi Daga Mummunan Kangi A Sudan
  • Wace Kungiya Ce Za Ta Lashe Kofin Zakarun Turai?
  • Bayan Shekaru 10 Madrid Da Barcelona Zasu Sake Yaɗuwa A Wasan Ƙarshe Na Copa Del Rey 
  • Yanzu Ne Lokacin Da Arsenal Ya Kamata Ta Lashe Kofin Zakarun Turai – Walcott
  • Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
  • Shin Manchester United Za Ta Iya Lashe Kofin Europa League?
  • Sayyid Fadhlullahi Ya Jaddada Muhimmanci Samar Da Makamai Ciki Har Da Kare Kasa Daga Dan Mamaya
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • Congo Da M23 Sun Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Wuta
  • Shawarar Tabbatar Da Tsaro A Duniya Ta Samar Da “Kyakkyawan Fata” Ga Duniya Mai Fama Da Tashin Hankali