Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Amurka Da Jakadan Sin A Burtaniya Sun Nuna Adawa Da Matakin Harajin Fito Na Ramuwar Gayya Da Amurka Ta Dauka
Published: 5th, April 2025 GMT
A ranar Alhamis ne, ofishin jakadancin kasar Sin da ke Amurka da jakadan Sin a Burtaniya Zheng Zeguang, suka bayyana matukar kin amincewa da harajin fito “na ramuwar gayya” da Amurka ta kakaba.
Suna masu nuni da cewa, Amurka ta sanar da karin harajin fito kan kayayyakin da ake shigowa da su daga kasashe da dama ciki har da kasar Sin, ta hanyar fakewa da abin da take kira ramuwar gayya, ofishin jakadancin Sin da ke Amurka ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, matakin ya saba wa ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, kuma ya saba wa ka’idojin tsarin cinikayya tsakanin bangarori daban-daban.
Kazalika, jakadan kasar Sin a Burtaniya, Zheng Zeguang ya ce, yin amfani da harajin fito a matsayin makami ya sabawa ka’idojin WTO, yana kuma yin illa sosai ga tsarin cinikayya tsakanin bangarori daban daban, kana yana haifar da babbar illa ga moriyar dukkan bangarori, jakadan ya bayyana hakan ne yayin da yake halartar bikin kaddamar ba da lamunin RMB na kasar Sin na farko kan ayyukan da ke maida hankali kan kiyaye muhalli wato green bond a birnin London.
Har ila yau, Zheng ya ce, kasar Sin tana adawa da karin harajin fito da Amurka ke shirin kakaba wa kan kasar Sin, kuma za ta dauki kwararan matakai don kare muradunta. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: harajin fito
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Kakabawa Kamfanonin Da Suka Hulda Da Iran Bangaren Man Fetur
A dai-dai lokacin da kasashen Amurka da JMI suke ci gaba da tattaunawa kan shirin makamashin nukliya ta Iran gwamnatin Amurka a jiya Laraba ta dorawa kamfanoni da mutanen da suke mu’amala da JMI a bangaren man Fetur takunkuman tattalin arziki. Da dama daga cikin wadannan kamfanoni na kasar China ne.
Jaridar ‘the Nation’ ta Amurka ta ce tun farkon wannan shekarar ne shugaban Trump ta farfado da takurawar tattalin arziki mafi muni a ka kasar Iran da nufin tilasta mata dawowa teburin tattaunawa ko kuma ta wagaza cibiyoyin Nukliyar kasar.
A halin yanzu dai kasashen biyu zasu ci gaba da tattaunawar ba kai tsaye ba, karo na hudu a birnin Roma na kasar Italiya a ranar Asabr mai zuwa. Kuma mai yuwa daga karshe su samarda sabuwar yarjeniya a tsakaninsu, kuma akwai yiuwar su kasa yin haka.
Wannan kuma zai faru ne idan Amurka ta bukaci JMI ta daina mu’amala da sinadarin Uranium kwatakwata ko kuma ta shigar da wata bukata wacce Iran ba zata amince ba.