HausaTv:
2025-04-27@16:17:37 GMT

Adadin Shahidan Gaza Sun Kai 50,669

Published: 5th, April 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiyar Falasdinawa ta sanar da cewa adadin shahidai a yankin na Gaza sun kai 50,669, yayin da wadanda su ka jikkata su ka kai 115,225.

Dangane da rahoton akan shahidan da ake samu a kowace rana kuwa,ma’aikatar kiwon lafiyar ta Falasdinawa ta ce, a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata an sami shahidai 60, wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 162.

Sanarwar ta kuma kara da cewa, da akwai wani adadin na shahidai masu yawa da suke kwance a kasa, ba a iya daukarsu balle a yi musu jana’iza ba, saboda yawansu, da kuma wadu dubbai da suke a karkashin baraguzai na gidajen da makaman HKI su ka rusa da mutane a cikinsu.

 A wani labarin daga Gaza, jiragen yakin HKI sun kai hari akan wata rumfa ta raba abinci ga Falasdinawa da suke fama a yunwa, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar mutane 3 a sansanin Khan-Yunus dake kudancin zirin Gaza.

Haka nan kuma sojojin na HKI sun kai hari akan gidajen mutane a cikin gain na Khan-Yunus da ya yi sanadiyyar shahadar muutm guda.

Wasu yankunan da ‘yan sahayoniyar su ka kai wa hare-hare sun hada  Qaizan Abu Rashwan dake kudu masu yammacin Khan-Yunus, da Hayyuz-Zaitun da kudu maso gabashin Gaza, sai kuma titin Sakkah a wannan  birni.

A gefe daya mutanen Gaza suna ci gaba da yin hijirar da aka tilasta su daga Hayyul-Shuja’iyyah, zuwa yammacin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen

Jiragen yakin Amurka sun kai jerin hare-haren a kan biranen San,a,Sa’adah da kuma Hudaidah na kasar Yemen.

Kamfanin dillancin labarun “Saba’a” na kasar Yemen ya nakalto cewa sojojin na Amurka sun kai hare-hare har sau uku a dutsen Naqam, wanda  yake gabashin birnin San’aa.

Kamfanin dillancin labarun na “Saba’a” ya kuma ce, jiragen yakin Amurka din sun kai hare-haren ne a tsakanin marecen jiya Laraba da kuma safiyar yau Alhamis.

Daga cikin wuraren da aka kai wa harin jiya da marecen da akwai Sahlin dake karamar hukumar Ali-Salim. Sau 6 Amurkan ta kai wa yankin hare-hare.

Da safiyar yau Alhamis kuwa jiragen yakin na Amurka sun kai hare-hare a gundumar Sa’adah.

Wasu yankunan da su ka fuskanci hare-haren su ne, al-tahita, dake kudancin gundumar Haudaidah, a yammacin kasar ta Yemen.

Amurka tana kai wa Yemen hare-hare ne saboda  bayar da kariya ga HKI, da zummar hana Yemen kai hare-hare akan manufofin ‘yan sahayoniya a ruwan tekun ” Red Sea”.

Kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ta bayyana cewa ba za ta taba daina kai wa HKI hare-haren ba har sai idan an daina kai wa Gaza hari. Bugu da kari ta sanar da cewa;za ta ci gaba da hana jiragen ruwa wucewa ta tekun “Red Sea” har zuwa lokacin da za a kawo karshen hana shigar da kayan agaji cikin yankin na Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
  •  Dakarun Kai Daukin Gaggawa Na Sudan Sun kashe ‘Yan Hijira Da Dama A Yankin Tekun Maliya
  • Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa Cibiyar Sojan Sama Ta “Nivatim” Hari Sau Biyu A Cikin Sa’o’i 24
  •  Adadin Wadanda Su ka Kwanta Dama A Gobarar Tashar Jirgin Ruwan Shahid Raja’i Sun Kai 21
  • An Gano Naira Miliyan 27.8 Da Suke Zirarewa A Albashin Kano
  • A Karon Farko A Tarihi Adadin Lantarki Da Sin Ke Iya Samarwa Ta Karfin Iska Da Hasken Rana Ya Zarce Wanda Ake Iya Samarwa Ta Amfani Da Dumi
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Jagora: Tafarkin Imaman Ahlul Bayti ( A.S) Na Gwgawarmaya Ne Da Jajurcewa
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen