HausaTv:
2025-04-26@22:41:29 GMT

Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba

Published: 6th, April 2025 GMT

Assalamu alaikum masu sauraro, sharhin bayan labarammu nay au zai yi magana kan cewa “Amurka ba zata taba zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da Falasdinawa ba” wanda ni tahir amin zan karanta.

A dai dai lokacinda rikicin gaza ya zama matsalar ta duniya a halin yanzu, da dama daga cikin masana suna ganin gwamnatin Amurka wacce ta kasance mai goyon bayan HKI na asali ba zata kuma zama mai shiga tsakanin don kawo karshen rikicinta da falasdinawa ba.

Dangane da wannan shafin yanar gizo mai suna “Alkhanadik’ ya rubuta wani sharhi dangane da yakin na gaza a jiya Asabar yana cewa, a dai dai lokacinda gwamnatin kasar Amurka ta kasance bangare babba a cikin haddasa matsaloli ga al-ummar Falasdinu na lokaci mai tsawo , ba zata kuma, zama a lokaci guda mai shiga tsakani don warware wannan matsalar wacce ta zama rikicin kasa da kasa ba.

Saboda ko way a san cewa wanda ya soma yaki ba zai zama mai kuma shiga tsakanin don samar da zaman lafiya ba.

Hakama kamfanin dillancin labaran ISNA na JMI ya nakalto cewa Donal Trump shugaban kasar Amurka yana son ya zama mai sulhuntawa tsakanin HKI da kuma falasdinawa, a rigimar da aka dauki shekaru fiye da 70 ana yenta, kuma gwamnatocin Amurka da suka shude har zuwa yau suna goyon bayan HKI, idan ba ma gwamnatin Amurka ba, da a halin yanzu babu HKI.

Masana sun kara da cewa gaskiyar al-amarin ita ce, a duk lokacinda Amurka da HKI sun yi maganan sulhuntawa ko kuma magance matsalar falasdinawa to kuwa, sai dai su kara rikita al-amarin Falasdinawa ta wani bangaren ne amma ba zasu taba gyara ba.

Don haka abinda muke gani a halin yanzu, ba bambancin sa da abubuwan da suka faru a baya ba, na tattaunawa a lokacinda ake ruwan wuta a kanku.

HKI tana kisan kiyashi a gaza, tana kuma ci gaba da rusa gidajensu da kuma duk wani gina a gaza, suna kashesu ta hanyar sasu yunwa, duniya tana gani, amma kuma a can washintong wasu suna maganar wai ana kokarin ganin yadda za’a kawo karshen rikicin.

Wannan ba sabon abu bane, an sha yin haka a baya. Na farko a samar da matsaloli sannan a yi amfani da shi, don tursasawa bangaren da ke da rauni don karban sharuddan da suka tsara.

Tun cikin watan Octoban shekara ta 2023 HKI tare da cikekken goyon bayan gwamnatin Amurka ta fara kissan kiyashi a Gaza, inda mafi yawan wadanda ake kashewar mata da yara ne, da kuma sunan kare kanta take wannan kissan. Manufarsu a wannan yakin a fili yake, wanda kuma shi ne share zirin gaza daga Falasdinawa. Don haka labaran da suke fitowa daga washinton a cikin yan kwanakin da suka gabata na cewa tana kokarin ganin an warware matsalar Falasdinawa da HKI, wata dasisa ce ta shirin neman wata kasa ko kuma wurin da zasu kwashi falasdinawa a Gaza, su kaisu can, sannan HKI ta shari zirin na Gaza ta ginawa yahudawan da take kwasowa daga kasashen yamma zuwa yankin gidana zama.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya  ba da umarnin gaggawa da a yi cikakken sauyi ga dabarun tsaron ƙasa, yana mai umartar shugabannin tsaro su ɗauki matakan gaggawa don daƙile ƙaruwar tashin hankali da kashe-kashe jihohin Borno, Filato, Binuwai, da Kwara.

Tinubu, wanda ya gana da shugabannin tsaro a Fadar Shugaban Ƙasa, ya ce dole ne a kawo ƙarshen kashe-kashe a jihohin da abin ya shafa.

“Ya isa haka,” in ji Shugaba Tinubu yayin da ya sake yin tir da kai hari ga ’yan Najeriya ba tare da wani dalili ba.

Mai ba da shawara kan harkokin tsaro na ƙasa (NSA), Nuhu Ribadu, ya shaida wa manema labarai cewa shugabannin tsaron sun yi wa shugaban ƙasa cikakken bayani kan halin da tsaro ke ciki.

Na ba ku wata 1 ku murƙushe ’yan ta’adda — Olukoyede ga sojoji Nijar, Mali da Burkina Faso sun kafa gidan rediyo na haɗin gwiwa NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Amfani Da Kafofin Sada Zumunta Wajen Haɓaka Kasuwanci

Ribadu ya ce Shugaba Tinubu ya ba da umarnin amfani da sabbin dabaru don magance matsalolin rashin tsaro.

Ya ce, shugaban ƙasar “ya ba mu damar zuwa mu sake yi masa bayani. Ya ɗauki lokaci mai tsawo muna masa cikakken kan abin da ke faruwa.

“Ko da ya yi tafiya ƙasar waje yana yawan tuntuba, yana ba da umarni kuma yana bin diddigin abubuwan da ke faruwa. A yau kuma mun sami damar sake yi masa bayani na tsawon awanni.

“Mun saurara, kuma mun karɓi sabbin umarni daga gare shi. Gaskiya, ya nace cewa mu yi aiki tuƙuru don maido da tsaro a ƙasa.

“Mun yi masa bayani kan abin da ya faru kuma muka tabbatar masa da jajircewarmu.

“Mun aiwatar da umarninsa, mun je wuraren da ake fama da rashin tsaro, kamar jihohin Filato da Binuwai da Borno, kuma mun ba shi ra’ayinmu saboda ya ba mu umarni mu je mu gana da hukumomin siyasa a can,” in ji shi.

Ribadu ya ce Tinubu ya jaddada buƙatar ƙara shigar da ƙananan hukumomi da gwamnatocin jihohi wajen magance al’amuran rashin tsaro.

“Matsalar rashin tsaro sau da yawa ba ta tsaya ga manyan matakai kawai ba. Ta ƙunshi ƙananan hukumomi. Su ne ke tare da mutane kai tsaye, musamman ma idan wasu ƙalubalen sun shafi matsalolin al’umma.

“Muna buƙatar yin aiki da al’ummomi  da ƙananan hukumomi da kuma gwamnoni. Shugaban Ƙasa ya ba da umarni cewa mu ƙara yin aiki da gwamnoni,” in ji shi.

Ribadu ya ce Shugaban Ƙasa ya “damu sosai” a taron kuma ya ce “abin ya isa haka.”

Ribadu ya ce maharan galibi suna kai hari ne kan ’yan ƙasa marasa galihu ta hanyar dasa bama-bamai da kuma kai hari kan wuraren da ba su da gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamaya Sun Yi Kasan Kiyashi A Zirin Gaza Da Kuma Ci Gaba Da Killace Falasdina  Cikin Masifar Yunwa
  • Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
  • Gaza: Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A  Yau Asabar
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Gargadin Munanan Sakamakon Da Zai Biyo Bayan Kashe Falasdinawa
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)
  • Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
  • Sojan HKI Ya Halaka A Gaza
  • Kasar Yemen Zata Aiwatar Da Abubuwan Mamaki Da Zasu Firgita Makiyanta Kuma Abokan Gaba
  • Ya isa haka: Tinubu ya umarci shugabannin tsaro su kawo ƙarshen kashe-kashe