Aminiya:
2025-04-07@02:43:46 GMT

Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya (2)

Published: 6th, April 2025 GMT

Alhamdulillah, a makon jiya ne muka fara gabatar da wannan rubutu wanda fahimtar malaman Mazhabar Malikiyya ce a kan azumin Sitta Shawwal a wani yunkuri na warware shubuhar da ake samu a tsakanin mabiya mazhabar a nan Najeriya.

Yayin da wadansu ke kokarin haramta azumin wadansu kuma nema suke yi su mayar da shi wajibi.

Muna fata da wannan dan rubutu da muka ciro daga shafin Cibiyar Imam Malik ta Intanet (Markazu Imam Malik) za a kawar da wannan takaddama.

Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya Manuniya kan azumin nafila bayan na Ramadan

1. Na ce ya dace a gabatar da biyan azumi ban ce ya wajaba daga farko ba.

Ya inganta a yi Sitta Shawwal kafin biyan azumin Ramadan; kalmar ya dace tana nufin wannan ne mafi kyau kuma wannan ne abin da Sheikh Bin Tahir ya ambata a fatawarsa, inda ya ce: “Ana gabatar da biya daga farko bisa aiki da ka’idar ‘Wajibi ne mafi dacewa da gabatarwa’.”

2. Na yi magana ce kan mas’alar a hali na bai-daya da aka saba, yayin da shi kuma ya yi ishara da hali na kebe yana mai togewa, ita ce rashin ikon biyan azumin da Sitta Shawwal a cikin watan, sai ya bayyana a wannan hali da cewar gabatar da Sitta Shawwal da ake tsoron kubucewarsa.

A nan akwai bambanci a tsakanin halayen biyu. Mafi dacewa gabatar da biyan Ramadan a kan azumin nafila.

Kuma a cikin halin gazawa da rashin ikon haka sai aka yi rahusa kan a yi azumin Sitta Shawwal kafin biyan Ramadan don kada su kubuce.

Fatawar Al-Jaza’iri

Fatawar Sheikh Abu Sharfuddin Al-Jaza’iri.

Shin azumin Sitta Shawwal makaruhi ne a wurin Malikiyya? Kuma mene ne hukuncin hada su a niyya daya da azumin ramuwa?

Amsa: Ga Allah muke neman dacewa; da sunan Allah Mai rahama Mai jinkai.

Godiya ta tabbata ga Allah Makadaici. Tsira da Amincin Allah su tabbata ga wanda babu wani Annabi a bayansa.

Bayan haka, lallai Allah Madaukaki Ya shar’anta a tare da kowace farilla wasu nafilfili don karfafa abin da zai iya aukuwa na nakasu ko sakaci.

Kuma daga cikin abin da Ya shar’anta a harshen AnnabinSa (SAW) akwai azumin Sitta Shawwal.

Imam Muslim da wadansu sun ruwaito cewa lallai Annabi (SAW) ya ce: “Wanda ya azumci Ramadan sannan ya bi shi da shida a Shawwal kamar ya yi azumin shekara ne.”

Sitta Shawwal a Shari’a

Don haka azumtar Sitta Shawwal shari’antacce ne kuma mandubi, sai dai Imam Malik (Allah Ya yi masa rahama) ya karhanta haka ne saboda wata illa da ya bayyana a cikin Muwadda.

Ya ce: “Lallai ni ban ga wani daga cikin ma’abota ilimi da fikihu na azumtarsu ba, kuma hakan bai riske ni daga wani daga cikin magabata ba.

“Kuma ma’abota ilimi suna karhanta haka suna tsoron kasancewarsa bidi’a da kuma riskar da Ramadan ga abin da ba ya cikinsa daga jahilai da masu jafa’i” (Muwadda, Juz’i na 1 shafi na 310).

Alkali Iyal ya ce, “Akwai yiwuwar Malik ya karhanta azumin ne a kan wannan dalili: mutum ya yi ittikadi a kan farilla ne.

“Amma wanda ya azumce su bisa fuskar da Annabi (SAW) yake nufi hakan ya halasta”( Ikmalul Mu’allim na Alkali Iyal, Mujalladi na 4 shafi na 139).

Amma fadin masu da’awar cewa Hadisin bai riski Malik ba, da’awa ce marar hujja, domin malaman Hadisi shida sun ruwaito Hadisin, kuma misalin wannan ba zai buya ga Malik ba, wanda shi ne babban malamin Madina kuma Shugaban Masu Hadisi “Ba zai jahilci wani abu daga wannan ba” (Al-Istizkar na Ibn Abdulbarri, mujalladi na 3 shafi na 380).

Amma hada su a niyya tare da niyya daya yana shiga abin da Fukaha’u suke kira da Tashrik (hadawa) a tsakanin ibadoji biyu da niyya daya.

A nan Malikiyya ba su amince da Tashrikin (hada) ramuwar azumi da azumin Sitta Shawwal bisa niyya daya ba, saboda hakan abin kyama ne a wurinsu don illar da ta gabata.

Amma sun amince da hadawar a Juz’iyyati na daban: daga ciki akwai hada azumin ramuwa da azumin Ashura ko Arfa ko hada alwala da wanka ko wankan Juma’a da na Janaba ko Tahiyyatul Masjid da Azhar ko raka’o’in Ihrami ko raka’o’in Dawafi tare da farilla…

A falala abin da ya fi shi ne:

1) Falala mai daraja ta daya: Mutum ya rama azumi yana mai gabatar da shi a kan Sitta Shawwal, kususan ga wanda ya yi niyyar ya biya a watan Shawwal, domin falalar Sitta Shawwal ba ta samuwa – bisa zahirin Hadisin da ya gabata – sai ga wanda ya biya abin da ke kansa na ranakun Ramadan da ya sha bisa uzuri.

A cikin wannan akwai fa’idoji biyu: Haduwar malamai a kan haka da kuma guje wa sabani.

2). Daraja ta biyu: Ya azumci Sitta Shawwal sannan ya bi su da ramuwar Ramadan a lokacin da ya so, kususan ga wanda ya yi niyyar ya jinkirta ramuwar zuwa bayan Shawwal.

Sabanin malamai

Kuma kan haka malamai sun yi sabani:

Hanafiyya sun halasta hakan kai-tsaye saboda lokacin yin Sitta Shawwal ya fi karanci a kan lokacin biya wanda shi ne shekara gaba dayanta. Don haka suka gabatar da wanda ya fi kunci a kan mai yalwa.

Hambaliyya sun haramta azumin nafila kafin biyan na Ramadan yanke.

Suka ce bashin Allah ya fi cancanta a biya. Kuma farilla ce ta fi dacewa a fara da ita a kan nafila.

Wannan a fili akwai tsanantawa a ciki, domin haramci yana bukatar dalili kuma a nan babu dalilin da za a dogara da shi.

Su kuwa Malikiyya da Shafi’iyya sun tafi ne a kan halalci tare da karhanci saboda abin da yake jerantuwa na shagala da tadawwu’i a kan ramuwar wajen jinkirta wajibi.

Kuma mafi alherin al’amari tsaka-tsakinsa – “Kamar haka Muka sanya ku al’umma matsakaiciya.”

Dalilin halascin abin da ya tabbata daga A’isha (RA) ta ce: “Yakan kasance a kaina akwai ramuwar azumin Ramadan, amma ban iya biya – sai a cikin Sha’aban.”

Wannan saboda shagaltuwa da Annabi (SAW). Buhari da Muslim suka ruwaito.

3). Daraja ta uku: Ya hada tsakanin ramuwar da Sitta Shawwal da niyya daya.

Wannan yana cikin hukuncin hada tsakanin nafila da farilla, kamar Sallar Tahiyyatul Masjid da Azahar ko tsakanin babba da karami kamar alwala tare da wanka.

Hakika malamai sun hadu a kan halascin haka a Wasa’il kamar alwala da wanka, ko wankan Juma’a tare da na Janaba, kamar yadda suka hadu a kan halascinsa a mas’ala daya ta Makasid, shi ne Kirani a Hajji, inda ake hada Umarah da Hajji da niyya guda.

Kuma da shi Annabi (SAW) ya yi Hajji a bisa magana mafi rinjaye. Sai suka yi sabani a bayan wannan cikin Makasid, misali hada Tahiyyatul Masjid da Azahar ko ramuwar azumi tare da Ashura.

Mun tsakuro wannan ne daga fatawar Sheikh Abdullahi Bin Tahir As-Susiy ta ran Juma’a 5 ga Shawwal, 1438 Bayan Hijira daidai da 30 /6/2017 Miladiyya.

Kayyade karhanci

Da wannan za mu ga cewa malaman Mazhabar Malikiyya da suka biyo baya sun kayyade karhancin yin azumin Sitta Shawwal da aka ruwaito Imam Malik (Allah Ya yi masa rahama) ya fadi a kan kada a sadar da su da azumin Ramadan wato nan take da an yi Sallar Idi.

Kuma kada mutumin da ake koyi da shi – shugaba ko babban malami – ya bayyana azumin.

Kuma kada ya kudurta cewa sunnoninsu ga Ramadan kamar sunnonin jeranta Ba’adiyya a Sallah ne.

Kuma kada mutum ya yi azumin dodar kwana shida a jere.

Suka ce idan aka aikata wadancan ne azumin ke zama makaruhi, amma in aka kiyaye su to azumin ya zama mustahabbi.

Allah Ya datar da mu ga abin da yake mafi daidai kuma Ya shiryar da mu ga tafarki madaidaici.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mazhabar Malikiyya Ramadan Sitta Shawwal azumin Sitta Shawwal Mazhabar Malikiyya Sitta Shawwal a a gabatar da a niyya daya

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Musulman Nijeriya Suka Gabatar Da Bikin Ƙaramar Sallah Cikin Matsin Tattalin Arziƙi

Shugaba Tinubu ya zanta da manema labarai bayan kammala Sallar Idi na karshen watan Ramadan a filin da aka gabatar da Sallar Idi na kasa a Abuja ranar Lahadi.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya fitar, shugaban ya bukaci ‘yan Nijeriya da kada su koma kan aikata abubuwan da su ba ta dace ba, a maimakon haka, ya bukace su da su dage wajen aiwatar da kyawawan dabi’un game da darusan da suka koya a watan Ramadan.

A cikin hudubar da babban limamin masallacin kasa dake Abuja, Dakta Abdulkadir Salman Sholagberu, wanda ya jagoranci Sallar ya gabatar, ya jaddada bukatar Musulmi su ci gaba da gudanar da ibadar da suka koya a Azumin watan Ramadan, wanda ya hada da koyar da rayuwar soyayya, hadin kai cikin adalci, kula da gajiyayyu da marasa galihu.

Ya jaddada cewa ya zama wajibi a ci gaba da gudanar da rayuwar ibada da tsarki da kuma biyayya ga Allah ko da a bayan Ramadan.

Dakta Salman ya bukaci al’ummar Musulmi da su zauna lafiya, da lumana, da kaunar kasa, ba tare da nuna wariya ba.

A gefe guda kuma, kungiyar Kiristoci ta Nijeriya CAN ta mika sakon taya murna ga al’ummar Musulmin Nijeriya a daidai lokacin da suke gudanar da bukukuwan karamar Sallah, yayin da a lokaci guda ta bukaci gwamnatin tarayya da ta binciki mummunan kisan gillar da aka yi wa mafarauta 16 a garin Uromi na jihar Edo.

A cikin sakon taya murna bayan kammala azumin watan Ramadan, shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh, ya jaddada muhimmancin bikin Idin karamar Sallah a matsayin lokacin tunani, da yin addu’a ga al’umma.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a jiya ne Shugaba Tinubu ya gudanat da bikin Sallah na farko a Abuja tun shekarar 2023.

Mataimakin Shugaban kasa Kashim Shettima, kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, Babban Mai Bai Wa Shugaban kasa Shawara Kan Harkokin Tsaro Nuhu Ribadu, da wakilan majalisar zartarwa ta tarayya, da sauran manyan jami’an gwamnati sun halarci Sallar.

A nasa bangaren, shugaban majalisar dattijai, Godswill Akpabio, ya taya al’ummar Musulmi barka da sallah, inda ya bukace su da su yi addu’ar samun hadin kan al’umma.

A wata sanarwa da ya fitar a Abuja ta hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, Hon. Eseme Eyiboh, Akpabio ya jaddada muhimmancin hadin kai tare da karfafa gwiwar Musulmi da su ci gaba da hadin kan kasa.

Hakazalika, gwamnan Jihar Ekiti, Biodun Oyebanji ya taya al’ummar Musulmin jihar da ma kasar murnar bukukuwan karamar Sallah.

A sakonsa na fatan alheri, mai dauke da sa hannun mai ba shi shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Yinka Oyebode, a ranar Lahadin da ta gabata, gwamnan ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin kwanaki 30 tare da jaddada bukatar ci gaba da gudanar da ayyukan ibada da ake nunawa a watan Ramadan duk shekara.

Gwamna Oyebanji ya hori al’ummar Musulmi da su rika amfani da koyarwar wata mai alfarma a duk wani aiki da za su gudanar, inda ya bukace su da mabiya sauran addinai su ci gaba da zama cikin soyayya da zaman lafiya da juna a matsayin ‘yan’uwa.

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya yi kira ga al’ummar jihar da su amfani da darasin da suka koya a cikin watan Azumin Ramadan, sannan su rungumi zaman lafiya da hadin kai.

Gwamnan, a wani jawabi da ya yi a ranar Lahadin da ta gabata jim kadan bayan Sallar Idin, ya taya al’ummar Musulmi murnar Sallah, a karshen Azumin watan Ramadan.

Ya bukaci al’ummar Musulmin Jihar Zamfara da sauran kasashen duniya da su yi zurfafa tunani kan sadaukar da kai ga Allah kamar yadda aka yi a cikin watan Ramadan.

Hakazalika, gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Yusuf, ya bukaci al’ummar Musulmi da su kiyaye dabi’u na hakuri, tausayi, hadin kai da aka koyar a cikin watan Ramadan.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature, ya fitar, ya jaddada muhimmancin sadaukarwa, tare da karfafa gwiwar ‘yan kasa da su tallafa wa marasa galihu da kuma samar da zaman lafiya a cikin al’ummarsu.

PDP, Atiku da Obi sun bukaci ‘yan Nijeriya da shugabanni su ji tsoron Allah da tausayi a tsakaninsu

Jam’iyyar PDP, Tsohon Mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar da tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Peter Obi, sun taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan mai alfarma, sun kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su kwatanta irin darusan da suka koya, kyawawaan dabi’un soyayya, hadin kai, zaman lafiya, hakuri, kamewa da kuma mika wuya ga Allah Madaukakin Sarki da sauran kyawawan dabi’u da suka shafi gudanar da mu’amalarsu ta yau da kullum.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labaranta na kasa, Hon Debo Ologungaba ya fitar, PDP ta bukaci ‘yan Nijeriya musamman masu rike da madafun iko a dukkan matakai da su sake sadaukar da kansu wajen gudanar da ayyukansu na nuna son jama’a bisa kyakkawan jagoranci, gaskiya, da rashin nuna wariya a dukkan ayyukansu tare da kawar da ayyukan cin hanci da rashawa, girman kai, magudi, da kaucewa nuna rashin sanin halin da al’umma ke ciki.

Mai magana da yawun babbar jam’iyyar adawar ya ce jam’iyyar ta damu matuka da yadda ‘yan kasar ke gudanar da bukukuwan Sallar Idi cikin hali na damuwa saboda wahalhalun da ba za a iya jure su ba na rashin kyawun mulkin jam’iyyar APC, wanda ya kara dagula al’amura a kasar cikin shekaru biyu da suka wuce.

Hakazalika, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a shekarar 2023, Mista Peter Obi, ya mika sakon fatan alheri ga Musulman Nijeriya, inda ya bukace su da su zama mdabbaka irin darusan da suka koya a Ramadan shi zai jagoranci rayuwarsu ta yau da kullum.

Mai magana da yawun Peter Obi, Mista Ibrahim Umar, ne ya mika sakon fatan alherin a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Obi a cikin sakon nasa ya ce, “Addu’armu itace Allah Madaukakin Sarki Ya karbi addu’o’inmu da azuminmu a yanzu da kuma ko da yaushe.

“Hakika abin farin ciki ne a gare ni in yi buda-bakin Azumin watan Ramadan tare da al’ummar Musulmi daban-daban a fadin kasar nan, samun albarkarmu da jin dadin junanmu ba wai kawai watan Ramadan kadai ba, har ma ya zama wani bangare na rayuwarmu ta yau da kullum.”

Ya yi addu’ar Allah ya sanya albarka a darusan da aka koya a watan Ramadan, wanda yin hakan shi zai sanya “soyayya a zukatanmu, zaman lafiya da hadin kai za su bunkasa a cikin al’ummarmu.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hanyoyin Warware Matsalolin Ma’aurata(1)
  • Abin da ya sa ba ma cin naman Akuya — Fulani
  • Jinkirin Fansho: PTAD Ta Fadi Dalili, Ta Ce Za a Biya Kudaden Wannan Wata
  • Kakakin APC na Ogun, Tunde Oladunjoye, ya rasu
  • Al-Azhar ta yi kira da a kama Netanyahu a matsayin mai laifin yaki
  • An haramta wa Akpabio da Natasha tattaunawa da manema labarai
  • Yadda Musulman Nijeriya Suka Gabatar Da Bikin Ƙaramar Sallah Cikin Matsin Tattalin Arziƙi
  • Kotun ƙoli ta sauke Julius Abure daga shugabancin jam’iyyar LP
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)