Amurka ta soke duk wata takardar izinin shiga kasar da aka baiwa ‘yan Sudan ta Kudu
Published: 6th, April 2025 GMT
Amurka ta sanar da soke duk wata takardar izinin shiga kasar wato (visa) da kasar ta baiwa duk wani dan Sudan ta Kudu.
Matakin a cewar Amurka na da nasaba ne da yadda Sudan ta Kudun ta ki karbar ‘yan kasarta da aka kora daga kasar.
A cikin wata sanarwa da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya fitar, ya ce ‘’ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta soke duk bizar kasar da ‘yan Sudan ta Kudu ke rike da a nan take.
Wannan shi ne irin matakin farko da aka dauka kan wasu ‘yan kasa a duniya tun bayan da Donald Trump ya koma kan karagar mulki a ranar 20 ga watan Janairu, a tsauraran manufofinsa na yaki da bakin haure.
Babban jami’in diflomasiyyar na Amurka ya kara da cewa lokaci ya yi da gwamnatin rikon kwaryar Sudan ta Kudu za ta daina samun wani tagomashi daga Amurka.
Kaddamar da dokar ta shige da fice na kasarmu yana da matukar mahimmanci ga tsaron kasa da amincin jama’a na Amurka.
Dole ne kowace kasa ta amince ta karbi yan kasarta da aka kora nan da nan inji gwamnatin ta Amurka inji shi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Za Ta Kara Sanya Harajin Fito Na Kaso 34% Kan Dukkan Kayayyakin Da Take Shigowa Daga Amurka
Kasar Sin ta sanar a yau Juma’a cewa, ta shigar da kara a gaban kungiyar cinikayya ta duniya WTO, kan matakin da Amurka ta dauka na kakaba harajin kwastam kan abokan cinikayyarta.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, ma’aikatar cinikayyar kasar Sin ta ce, harajin kwastam da Amurka ta kakaba, ya matukar take halaltattun hakkoki da muradun kasashe mambobin WTO, kuma ya matukar dagula ka’idojin tsarin cinikayya tsakanin bangarori daban daban da kuma tsarin tattalin arziki da cinikayyar kasa da kasa.
Bugu da kari, hukumar harajin kwastam ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta bayyana a yau Juma’a cewa, kasar Sin za ta kara sanya harajin fito na kaso 34% kan dukkan kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, farawa daga ranar 10 ga watan Afrilun nan da muke ciki. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp