Pezeshkian ya soki barazanar Amurka kan kasarsa game da tattaunawar nukiliya
Published: 6th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya soki abunda ya danganta da barazanar Amurka ga Teheran, yana mai cewa kasarsa a shirye take ta shiga tattaunawa ta hakika ba tare da barazana ba.
“Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman tattaunawa ta gaskia, a yayin da suke barazana ga Iran a daya bangaren kuma suna neman yin shawarwari,” in ji Pezeshkian a ranar Asabar.
“Idan kuna neman shawarwari, to me yasa kuke yin barazana? A yau, Amurka ba wai kawai ta wulakanta Iran ba har ma da duniya, kuma wannan hali ya saba wa bukatar tattaunawa,” in ji shi.
Kalaman na Pezeshkian sun zo ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira ga Tehran da ta shioga shawarwari kai tsaye kan shirinta na nukiliya yayin da ya yi barazanar jefa bama-bamai a Iran idan diflomasiyya ta gaza.
A ranar Lahadin da ta gabata, ne Trump ya sake yi wa Iran barazanar kai harin bama-bamai da kuma lafta mata takunkumai masu tsauri a karo na biyu idan ba ta cimma matsaya da Washington ba kan shirinta na nukiliya, a yayin da kuma Amurka ta kara tura karin jiragen yaki zuwa yankin.
Tunda farko Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araghchi ya sake nanata shirin Tehran na shiga shawarwarin da Amurka kan shirinta na nukiliya na zaman lafiya, saidai yana mai gargadin cewa barazanar Amurka na dagula halin da ake ciki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Taron Dandalin Tattaunawar Afirka Ta Yamma Karo Na Farko A Senegal
A nasa bangare kuma, firaministan kasar Senegal Ousmane Souko ya bayyana cewa, kasar Senegal tana son hadin gwiwa da cibiyar nazarin ilmin kimiyyar zamantakewar al’umma ta kasar Sin don kara cudanyar juna da gudanar da ayyukan nazarin ilmi tare, baya ga samar wa kasashen dake yammacin nahiyar Afirka dabarun neman samun ci gaba.
Bugu da kari, shugaban kwalejin nazarin hukumomin kasar Senegal ya ce, aikin kulla yarjejeniyar kafa cibiyar nazarin Sin da Afirka cikin hadin gwiwa, ya shaida yadda hadin gwiwar kwararru a tsakanin Sin da Afirka ya kai wani sabon matsayi. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp