Rasha za ta bude ofishin jakadanci a Nijar nan ba da jimawa ba
Published: 6th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Nijar ya sanar da cewa nan ba da jimawa ba za a Rasha za ta aika tawagar diflomasiyya a Nijar.
Nijar ta tabbatar da aniyar ta na karbar bakuncin ofishin jakadancin Rasha a karon farko cikin sama da shekaru talatin, in ji ministan harkokin wajen kasar ta yammacin Afirka, Bakari Yaou Sangare a ranar Alhamis.
Bayanin ya fito ne yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Moscow bayan tattaunawa tsakanin ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov da takwarorinsa na kasashen Nijar, Mali, da Burkina Faso.
M. Sangare ya bayyana cewa, a halin yanzu Nijar na neman wurin da ya dace domin gina ofishin jakadanci na tawagar diflomasiyyar Rasha a kasar, ya kara da cewa Yamai na fatan nan ba da jimawa ba Moscow za ta nada jakada.
‘’Mun rufe ofishin jakadancinmu a Rasha a cikin 1990s, amma daga baya mun gane cewa wannan kuskure ne,” in ji shi.
Lavrov ya tabbatar da cewa kasashen biyu suna kan hanyar dawo da wakilcin diflomasiyya. “A nan gaba kadan, tare da taimakon ku, za mu kammala dukkan ayyukan don dawo da ofishin jakadancinmu.
Kuma tabbas za mu yi hakan a cikin shekarar nan ta 2025,” in ji ministan harkokin wajen Rasha.
A farkon wannan shekara, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta tabbatar da cewa, Moscow na da niyyar bude sabbin ofisoshin jakadanci a kasashen Afirka da dama da suka hada da Nijar, Saliyo, da Sudan ta Kudu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro
Da ya ke magana kan ziyarar tawatar NBTE, Rector ɗin ya ce aikin sahalewa na da matuƙar muhimmanci domin gano irin ƙoƙari da azamar makaranta a cikin shekaru biyar da suka gabata da nufin tabbatar kayan koya da koyarwa da malamai suna nan kan tsarin da aka amince da tafiyar da su tun da farko.
Ya tabbatar da cewa kwasa-kwasai har guda 78 ne jami’an NBTE suka nazarta a yayin wannan ziyararz, “Tawagar sun gama aikin su na ziyarar, yanzu haka muna zaman jiran sakamakon bincike da bin sawun nasu ne,” ya ƙara shaida.
A nata ɓangaren, Dakta Fatima Umar, daraktan shirye-shiryen kwalejoji kuma jagorar tawagar na NBTE, ta buƙaci kwalejin Kimiyya da fasaha na gwamantin tarayya da ke Bauchi da ya maida hankali wajen magance matsalolin gine-gine da kuma giɓin ma’aikata.
Da take samun wakilcin Adesina Oluade, ta jero sauran matsalolin da ta gano kamar ƙarancin littafai na ɗalibi, mujallu na ilimi, rashin samar da wutar lantarki yadda ya kamata, inda ta ce bangarorin na buƙatar daukan matakan gaggawa.
Umar ta jaddada cewa tsarin sahalewa na da nufin ƙarfafa tabbatar da samar da ilimi mai ingancin da kyautata aiki, inda ta sha alwashin cewa kwamitin zai cigaba da yin gaskiya da adalci a yayin aikinsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp