HausaTv:
2025-04-27@16:59:14 GMT

Guteress : ba wadan zai ci ribar yakin cinikayya

Published: 6th, April 2025 GMT

Sakatare janar na majalisar dinkin duniya ya ce ba wanda zai ci ribar yakin cinikayya a yayin da ake ta cacar baka kan harajin fito da shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa duniya.

 Antonio Guitess ya yi wannan gargadin ta bakin kakakinsa inda ya yake bayyana cewa, “ba wanda ke yin nasara a yakin na cinikayya.

” Yana mai cewa, a yayin da ake samun karuwar adawa daga sassa daban daban, shugaban Amurka Donal Trump a ranar Laraba ya rattaba hannu kan wani umarnin zartarwa kan abin da yake kira “harajin fito na ramuwar gayya,” wanda ya sanya kashi 10 cikin dari na mafi karancin harajin fito, da karin sama da haka kan wasu abokan cinikayyar kasar.

A wani batun kuma, taron MDD kan cinikayya da ci gaba wato UNCTAD, ya yi gargadi a cikin wata sanarwa a ranar Juma’a cewa, harajin fito da Amurka ta sanya zai cutar da kasashe masu rauni, kana “tsarin cinikayya na duniya ya shiga wani mataki, wanda ke yin barazana ga ci gaba, da zuba hannun jari, musamman ga kasashe masu rauni,” yayin da manyan kasashe masu karfin tattalin arziki ke shirin sanya sabbin harajin fito a nasu bangare a matsayin ramuwar gayya ga matakin na shugaban Amurka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: harajin fito

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara

A watan Janairu kawai, marigayi shugaban ‘yan fashin daji, Isuhu Yellow, ya sanya harajin naira miliyan 172.7 a kauyuka 25, ciki har da bukatar amfanin gona.

 

A misali, an kakaba wa kauyen Gijinzama harajin naira miliyan 8.5, Dakolo naira miliyan 5 da buhunan wake 20, da Kibari, Kunchin Kalgo naira miliyan 20, Sungawa naira miliyan 15, da Yalwa naira miliyan 2.7, da dai sauransu.

 

Ba da jimawa ba, wani shugaban ‘yan fashin dajin nan, Dogo Gide, ya bukaci a biya naira miliyan 100 daga wasu al’ummomi 23 da ke karamar hukumar Tsafe, lamarin da ya sa jama’a suka kauracewa gidajensu.

 

Al’ummomin da abin ya shafa sun hada da Kunchin-Kalgo da aka nemi naira miliyan 20 daga wajensu, Sungawa naira miliyan 15, Rakyabu naira miliyan 15, da Kwaren Mai-Saje naira miliyan 10.

 

A ranar Lahadi, 20 ga Afrilu, ‘yan bindiga sun sake neman naira miliyan 60 daga mazauna kauyen Dankurmi a karamar hukumar Maru.

 

Wani mazaunin kauyen Kwalfada a karamar hukumar Tsafe wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya tabbatar da cewa ‘yan garkuwa da mutanen sun kakaba wa rayuka da dama haraji a yankin.

 

Ya ce, miliyoyin naira ne masu garkuwan suka nema a hannun jama’a ko kuma su kawo musu farmaki.

 

Wani mazaunin kauyen Dan Jibga, Mai suna Muhammad Dogo, ya ce ‘yan fashin daji sun sanya harajin naira miliyan 10 ga al’ummar Gama Lafiya bayan kashe wasu mutum biyu a ranar Lahadi da Litinin.

 

Dogo ya ci gaba da cewa, sauran kauyukan da harajin ya shafa sun hada da Unguwar Tofa naira miliyan 26.6, Makera naira miliyan 15, Sungawa naira miliyan 20, Rakyabu naira miliyan 7, Yalwa naira miliyan 8, Kwarin Mai Saje naira miliyan 11, Langa-Langa, inda harajin ya kai tsakanin naira miliyan 20 zuwa naira miliyan 30.

 

Ya kara da cewa ‘yan fashin dajin sun kwace kauyukan Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga, da Bilbis.

 

Wani mazaunin garin Mara da ke karamar hukumar Maru, Malam Ibrahim Maru, ya koka da yadda matsalar ‘yan fashin dajin ke ta kara ta’azzara a yankin Maru a ‘yan kwanakin nan.

 

Ya ce, “Hanyar Talata Mafara zuwa garin Maru ta zama tarkon mutuwa ga matafiya da direbobin wanda sun daina amfani da hanyar bayan karfe 4 na yamma.

 

“Da zarar karfe 4 na yamma ya yi zai yi wuya a samu direban da ke son daukar fasinjoji daga Maru zuwa Talata Mafara, kwanan nan na yi tattaki daga Talata Mafara zuwa Maru domin ziyarar jaje, amma da isa Maru, sai aka ba mu shawarar mu koma.

 

“Wannan hanyar ba ta da tsaro, ‘yan bindiga sun ci gaba da ayyukansu, suna gudanar da ayyukansu ba dare ba rana, sun yi garkuwa da mutane da dama, ciki har da mata da yara, a kauyuka daban-daban, kuma suna sanya haraji a kan al’ummomi da dama.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Babban Bankin Sin: Harajin Amurka Ya Jefa Kasuwanni Da Kasashe Masu Tasowa Cikin Hadari
  • Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
  •  Kotun Tsarin Mulki Ta Gabon Ta Tabbatar Da Nasarar Nguema A Zaben Shugaban Kasa
  • ‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Natenyahu Ba Zai Hadi Fada Da Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ba
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare Hare Kan Yakuna 4 A Kasar Yamen
  • Amurka Ta Fara Dandana Kudar Manufar Kakaba Harajin Kwastam
  • Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam
  • Amurka Ta Kai Hare-hare Akan Birane Mabanbanta Na Kasar Yemen