Guteress : ba wadan zai ci ribar yakin cinikayya
Published: 6th, April 2025 GMT
Sakatare janar na majalisar dinkin duniya ya ce ba wanda zai ci ribar yakin cinikayya a yayin da ake ta cacar baka kan harajin fito da shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa duniya.
Antonio Guitess ya yi wannan gargadin ta bakin kakakinsa inda ya yake bayyana cewa, “ba wanda ke yin nasara a yakin na cinikayya.
” Yana mai cewa, a yayin da ake samun karuwar adawa daga sassa daban daban, shugaban Amurka Donal Trump a ranar Laraba ya rattaba hannu kan wani umarnin zartarwa kan abin da yake kira “harajin fito na ramuwar gayya,” wanda ya sanya kashi 10 cikin dari na mafi karancin harajin fito, da karin sama da haka kan wasu abokan cinikayyar kasar.
A wani batun kuma, taron MDD kan cinikayya da ci gaba wato UNCTAD, ya yi gargadi a cikin wata sanarwa a ranar Juma’a cewa, harajin fito da Amurka ta sanya zai cutar da kasashe masu rauni, kana “tsarin cinikayya na duniya ya shiga wani mataki, wanda ke yin barazana ga ci gaba, da zuba hannun jari, musamman ga kasashe masu rauni,” yayin da manyan kasashe masu karfin tattalin arziki ke shirin sanya sabbin harajin fito a nasu bangare a matsayin ramuwar gayya ga matakin na shugaban Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harajin fito
এছাড়াও পড়ুন:
Nazarin CGTN: An Bukaci Kasa Da Kasa Su Bijirewa Cin Zali Daga Amurka
Nemi adalci maimakon babakere. Cin zali ta hanyar kakaba haraji da Amurka ke yi, ya haifar da suka da adawa da martani daga kasashe da dama. Takarda mai dauke da matsayar kasar Sin da aka fitar dangane da cin zalin ta samu goyon bayan daga kasa da kasa. Sakamakon wani nazari da kafar CGTN ta gudanar tsakanin masu amfani da intanet a fadin duniya, ya nuna wadanda suka amsa nazarin na kira ga kasashen duniya su hada hannu su dauki mataki domin bijirewa salon cin zali irin na Amurka, su kare hakkokinsu da kuma tsarin cinikayya da tattalin arziki na duniya.
Bisa fakewa da daidaito da adalci, Amurka na son cin riba daga faduwar wasu, inda take sanya muradunta sama da na al’ummar duniya. Kasar Sin na adawa da hakan tana mai bayyana neman ci gaba a matsayin ‘yanci na bai daya na dukkan kasashe ba na wasu ‘yan tsiraru ba.
Game da hakan, kaso 86.9 na masu bayar da amsa sun yi ammana cewa, matakan martani da kasashe suka dauka game da matakan Amurka na cin zali ta hanyar haraji, abu ne da ya halatta na kare muradunsu. Har ila yau, kaso 89.2 sun yi kira ga karin kasashe su dauki karin matakai na kandagarki game da batutuwan cinikayya da Amurka, suna masu bayyana adawa da yadda Amurka ke yin gaban kanta wajen cin zali a dandalin hadin gwiwar kasa da kasa kamar hukumar kula da cinikayya ta duniya (WTO). (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp