Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar Kano Rano LGA:

Alhamdulillah mun yi bikin sallah lafiya kalau a garin Rano kamar yadda muka saba duk shekara kowa yana uzurinsa kamar yadda aka saba lafiya. Alhamdulillah an yi ziyarce-ziyarce lafiya gidajen ‘yan’uwa da surukai da abokan arziki da kuma haduwa da tsofaffin dalibai.

Gaskiya sai godiya duba da yadda ake cikin tsadar rayuwa da wani irin hali na kuncin rayuwa a wannan a kasa ta mu sai dai mu a yankinmu na karamar hukumar Rano muna cikin alhinin kisan gillar da aka yi wa ‘yan’uwanmu a yankin kudu a jihar Edo ba zamu tava manta wannan aika-aika da aka yi mana ba Allah ya isar mana, Allah ya sa mudace Allah yasa mun yi ibadu karvabbu Allah ya maimaita mana masu amfani.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar Kaduna:

Bikin sallah ya kayatar da mu sosai sai dai wasu ba kamar yadda suka saba duk shekara ba, musamman yadda sallar ta zo ba tare da wasu sun kammala shiri ba. Na ziyarci ‘yan’uwa na na kusa da na nesa kamar Babbar Yayata, Kawu na, Aunty na, dan har garin Kano mun ziyarta, sai wuraren shakatawa, gidajen tarihi, da kuma gidan Sarki. Sallar bana za a ce da ita ma sha Allah Alhamdulillahi, an yi ta cikin zaman lafiyya da kwanciyyar hakali, mun yi kallon hawa.

Sunana Aminu Adamu, Malam Maduri A Jihar Jigawa:

Alhamdullilah Ma sha Allah, hakika mun gudanar da bikin sallar idi da shagulgulan bikin sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, al’umma sun yi hidimar sallah daidai gwargwado duk da halin da ake ciki na matsin tattalin arzikin da tsadar rayuwa, fatan mu Allah ya karvi ibadar mu bakidaya. To maganar zuwa ziyara hakika mun ziyarci gidajen ‘yan’uwa da abokan arziki an gaisa an yi zumunci sosai kai har ma mun samu damar zuwa garuruwan ‘yan’uwa dake nesa domin sada zumunci. To batun sallah sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah tunda mun samu damar gudanar da sallah cikin nutsuwa da kwanciyar hankali domin koda ba a samu damar yin hidima mai yawa ba tunda aka samu damar gudanarwa cikin lumana dole mu godewa Allah daya ba mu wannan dama, daga karshe nake kara addu’ar Allah ya karvi ibadar mu ya yafe mana kura-kuran mu don darajar fiyayyen halitta manzon Allah (S.A.W).

Sunana Hafsat Yusuf Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto:

Hidimar wannan sallar ta zamo mai kayatarwa a garin mu duk da matsalar tsaron da ake fama da ita a yankin, mun kai ziyara ga ‘yan’uwa kuma mun hadu da wadanda muka dade ba mu hadu da su ba, abun akwai burgewa. Daga karshe ba abun da zan ce sai Alhamdulillah Allah ya maimaita mana.

Sunana Yasar Saleh Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Yadda bikin sallah yake kasancewa a garin mu sai mu ce Alhamdullilah Ma sha Allah. Da zarar gari ya waye kowa da kowa zai fita filin idi dan gabatar da sallah da an sakko za ai ta kai ziyara zuwa gidan ‘yan’uwa da abokan arziki; yayye, kanne da ‘yan’uwa da abokan arziki. To sai godiyar Allah amma kam ta zo wa mutane da yanayi na tsadar rayuwa da matsin tattalin arzikin da muke fama da shi amma duk da haka Alhamdullilah tun da mun samu damar gudanar da bikin cikin nutsuwa da kwanciyar hankali.

Sunana Fatima Ibrahim Jihar Katsina:

Bikin sallah dai a unguwar da nake ya kasance abu ne mai ban sha’awa, mun je gurare da dama kamar gidan zoo, gurin wasa, gidan ‘yan’uwa da abokan arziki da gidan makama. A gaskiya dai wannan sallar za a iya cewa ta zo kwatsan dan wadansu basu tanadi dinkin sallah ba da kuma lalle da sauransu, ni dai na samu nayi da wuri komai kalau a wajena.

Sunana Fatima Nura Kila, A jihar Jigawa:

Alhamdulillah mun yi sallah lafiya inda kowa yake cikin farin ciki a wannnan rana ta sallah duk da yanayin da ake ciki, amma mutane sun yi ado daidai wadaitar kowa, fatanmu Allah ya nuna mana wata sallar. Alhamdulillah mun yi ziyarar ‘yan’uwa da abokan arziki mutanan da aka dade ba a hadu ba mun kai musu ziyara Yayin da kowa yake farin ciki da ziyarar juna. Wannnan sallar sai dai mu ce Alhamdulillah domin an samu zaman lafiya mun yi ta cikin nutsuwa,walwa da kaunar juna, Ubangiji ya karvi ibadunmu ya kai mu wata shekarar mai albarka ya sa muna raye.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Arziki yan uwa da abokan arziki cikin nutsuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu

A wannan makon Aminiya ta samu tattaunawa da shahararren jarumi a masana’antar fina-finan Hausa ta Kannyood, Malam Inuwa Ilyasu, wanda ya shafe sama da shekara 40 yana harkar wasan kwaikwayo. Ga yadda tattaunawar ta kasance:

Gabatar da kanka?

To da farko dai sunana Inuwa Ilyasu.

Yaushe ka fara harkar fim?

Gaskiya dai kusan da ni aka fara yin fim kuma lokacin da muka fara yi, mun fara da yin tunanin ya za mu yi saboda kafin nan ai akwai wasan daɓe da muka fara yi.

A wancan lokaci muna faɗakarwa ta wasan kwaikwayo kusan tun wajejen 1970. Daga nan muka fara tunanin ta yaya za mu yi ƙoƙarin mu ma mu fara yin irin namu.

Yawancin fina-finanka kana fitowa ne a matsayin malami, kana faɗakarwa ko bayar da shawara a addinance. Wannan matsayin kai kake zaɓa ko kuwa masu shirya fim ne suke ba ka?

A’a ba ni na zaɓar wa kaina ba.

Idan na fahimce ka, an duba cancanta da kuma wanda aka gani zai iya bayar da abin da ake so ake ɗora ka a kai?

Yauwa, ana yin sa’a ce dai za ni ce ta tarar da mu je, domin ni daman dalilina na yin wasan kwaikwayo shi ne, saboda in samu in cusa aƙida ta addinin Musulunci da tarbiyartarwarsa da kuma cusa al’adarmu da ɗabi’unmu ga matasa masu tasowa. Misali, ai ka ga irin yadda wasu masu fim ɗin Indiya suke cin karensu babu babbaka.

Daga lokacin da ka fara wasan daɓe zuwa yadda ka juya zua yin fim, shin kana ga saƙonnin da kake son isar wa jama’a suna tasiri wajen faɗakarwa ?

Alhamdulillahi, ana samun nasara Insha Allahu, saboda mutane da yawa in na haɗu da su ko kuma ma wasu su ne za su neme ni, su yi yabo saboda Allah Ya sa sun ci karo da wata faɗakarwa da na yi a wani shirin da ta yi tasiri matuƙar gaske ga rayuwarsu.

Ka shafe sama da shekara 40 a sana’ar harkar fim, ko kai ma ka fara tunanin kafa wani kamfani da idan ka yi fim za ka riƙa ɗorawa a manhajar Youtube kamar yadda wasunku ke yi halin yanzu?

To ni irin wannan ba ya cikin tunanina. Kamar yadda na gaya maka a baya, mun fara yi ne da manufa, kuma muna yi ne domin faɗakarwa ga jama’a a ƙarƙashin ƙungiya da na faɗa mai suna “Dabo”. Haka kuma mun samu nasara, domin wasu daga cikin waɗanda suke a Kannywood ɗin cewa suke yi daga kallon fim ɗin da muke yi, suka koya. Wasu kuma daga irin faɗakarwar da ake yi a fim ta ba su sha’awa har su ma suka shigo matsayin masu yin fim. Wani kuma zai ce shi fim ya kalla, ya sa masa soyayyar abin a zuciyarsa, Alhamdulillahi an samu ci gaba sosai da nasara.

Kamar ta wace gaɓa nasarorin da aka samu?

Gaɓoɓin da dama, saboda za ka samu wasannin da muka yi, wasu suka kalla za su ɗauki darasin rayuwa, sannan muna harkar arziki da jama’a, ana ta nuna mana soyayya ba wata matsala. Sannan idan ma suna muke so mu samu, mun samu. Kai wasu ma na raɓe da mu, sun samu sannan akwai da dama da suke son su samu dama kamar yadda muka samu, amma ba su samu ba.

Wato dai fim ɗin duk da ka fito rawar da kake takawa da aka ba ka ana amfana da ita a kan duk abin da ka faɗakar ko ka a addinance ko a al’adance?

Eh, an samu ci-gaba sosai kuma Alhamdulillahi.

Ya kake kallon ƙalubalen da ake samu a tsakanin masu harkar fim?

Ban fahimce ka ba.

Irin ’yan matsaloli da ka taso tsakanin mawaƙa ko masu yin fim na baya-bayan nan da ake zargin su da wuce gona da iri?

Irin waɗannan abubuwan gaskiya muna ta yaƙin su a matsayinmu na dattawa. Amma ka san ɗan-adam sai da hikima.

Wace shawara kake da ita ga Masana’antar Kannywood da kuma masu nufin nan gaba su shigo ta, lura da cewa yanzu ka zama uba a cikinta tun daga kan hukuma da kuma jarumai?

Eh to akwai buƙatar sake duba inda hukuma za ta shigo ta gyara a cikin harkar, domin muna magana ne a kan addini da tarbiyya, musamman ta Musulmi. Ya kamata a ce gwamnati da ta kafa wannan hukuma ta tallafi to kuma ta duba hanyar da za ta tallafa wa wannan harkar saboda harkar fim tana bayar da dama ga matasa ta samun sana’a. Haka kuma tana hana zaman kashe wando. Sannan kuma ana amfani da fim wajen kawar da wasu miyagun abubuwa da suke faruwa a cikin al’umma, ta yadda ba sai an fito, ana kokawa ko kama mutane ba don yin gyaran. Saboda mu ƙalubale gare mu, mu tabbatar masu kallo za su gamsu da abin da muke yi kuma su faɗaka.

Ban sani ba ko akwai wani saƙo da kake son ka isar?

Saƙona shi ne, kowa lallai yana da buƙatar ya sanya hannu wajen tallafa wa wannan harka ta fim, saboda ta shafe shi a abin da ya shafi addininsa da al’adarsa. Don haka ya kamata kowa ya duba ta ina zai taimaka yadda za ta inganta, ta dace da waɗannan muhimman abubuwa.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ribar Wasu Manyan Kamfanonin Masana’antun Sin Ta Karu Da 0.8% a Farkon Watanni Uku Na Bana
  • Rasha Ta Fara Aika Isakar Gas Zuwa Kasar  Iran Ta Azarbaijan Don Sayarwa A Kasuwannin Duniya
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Siriya Ya Bukaci MDD Ta Dagewa Kasarsa Takunkuman Tattalin Arziki
  • Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu
  • Kwamitin Tsakiyar JKS Ya Gudanar Da Taron Nazarin Tattalin Arziki
  • Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
  • Jigawa Ta Bude Sabon Babi: Maniyyata Za Su San Masaukansu Tun Daga Gida Najeriya
  • Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)
  • Gwamna Dauda Lawal Ya Nada Amirul Hajj Bana
  • Yayin Da Ake Fuskantar Daminar Bana: Sabbin Hare-hare Na Barazana Ga Shirin Wadata Kasa Da Abinci