An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36
Published: 6th, April 2025 GMT
Da farko Kinjal Lathi, ta fara cire rai daga samun haihuwa da jin daɗin zama a matsayin uwa saboda cutar borin jini ta thalassemia da take fama da ita.
Dole a riƙa yi mata mata ƙarin jini duk bayan mako biyu, sannan dole ta bi wasu ƙa’idojin cin abinci da magunguna.
Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya (2) ’Yan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi domin amsa tambayoyiBayan kuma cutar da take fama da ita, akwai kuma ƙalubalen ɗaukar ciki da take fama da shi.
‘’Ina ganin fuskar ’yata sai na manta da duk wata wahalar da na sha a sanadiyar ɗaukar ciki da naƙudar,” in ji Kinjal Lathi, daga yankin Ahmedabad da ke Jihar Gujarat a kasar Indiya, inda ta ƙara da cewa, “ni da mijina mun sha kuka.”
“Akwai barazana babba ga uwa da abin da ke cikinta. Amma na yanke shawarar cika burina na zama uwa,” in ji Kinjal, kamar yadda majiyar BBC ta ruwaito.
Sai dai an yi wa Kinjal ƙarin jini sau 36 lokacin da take da ciki, amma kuma ta haifi lafiyayyiyar jaririya a ranar 12 ga watan Yulin 2019.
Ko bayan haihuwar ma, sai da aka ci gaba da yi wa Kinjal mai shekara 25 ƙarin jini, inda ta ce wasu lokutan ma ana yi mata ƙarin jinin ne a yayin da take shayar da jaririyarta.
Sannan kuma wani abun farin cikin shi ne ’yarta ba ta gaji cutar ba.
Wata ƙwayar halitta ce take samun matsala, wadda ke hana cuɗanyar jini da iska domin samar da jinin da ake kira haemoglobin, wanda shi ne yake zagayawa da jini mai ɗauke da sinadarin protein a jiki.
Yaya cutar thalassemia ke shafar juna biyu?
Ba a cika masu irin wannan cuta irin Kinjal suna haihuwa lafiya ba, kamar yadda likitan yara, Anil Khatri, wanda yake cikin kwamitin kar ta kwana na yaƙi da cutar ya bayyana.
Ya ce, bai taɓa ganin haka ba sama da shekara 30 da ya yi yana aikin kula da masu cutar ba, inda ya yi jinyar masu cutar sama da guda 100.
Akwai masu cutar kusan miliyan 270 a duniya, kamar yadda ma’aikatar lafiya da walwalar iyali ta bayyana.
Akwai na’ukan cutar da dama, ciki har da wadda ake kira ‘Hemoglobin H disease’, wadda ita ma ta kasu kashi biyu, wato nau’in alpha da beta – nau’in beta (TM) ce ta fi illa.
A Indiya akwai yara kimanin 100,000 zuwa 150,000 da suke ɗauke da cutar.
Ɗaukar ciki abu ne mai wahala ga mata masu cutar, kamar yadda likitan haihuwa, Umar Khatri ya bayyana.
Idan mace na da juna biyu, jininta yana ƙaruwa, wanda hakan ya sa jikin ke buƙatar ƙarin sinadarin ‘iron’ domin tallafa wa kai iska zuwa ga jariri.
“A ƙa’ida muna kiran mata masu juna biyu ne, su zo a duba su aƙalla sau ɗaya a wata.
“Amma ita Kinjal tana zuwa ne duk kwana 15, wanda shi ne karo na farko da muka samu hakan,” in ji Khatri.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Indiya ƙarin jini ƙarin jini kamar yadda
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Na Nuna Damuwa Sosai Kan Harin Intanet Da Aka Kai Mata
A jiya Alhamis 3 ga wata ne, cibiyar daukar matakan gaggawa kan matsalolin kwayar cutar na’ura mai kwakwalwa ta kasar Sin, gami da ofishin gwajin ayyukan fasahohin magance kwayar cutar na’ura mai kwakwalwa na kasar, suka bullo da wani rahoto, kan binciken hare-haren yanar gizo da wasu kasashen waje suka kai kan tsarin adana bayanan gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta nahiyar Asiya karo na 9 da aka yi a birnin Harbin, babban birnin lardin Heilongjiang da ke arewa maso gabashin kasar Sin a shekara ta 2025, gami da wasu muhimman ababen sadarwa dake lardin na Heilongjiang, inda ya shaida yadda kasar Amurka ta kaddamar da hare-haren intanet, kan tsarin adana bayanan gasar wasannin motsa jiki ta lokacin hunturu ta Asiya karo na 9 da aka yi a birnin Harbin, gami da wasu muhimman ababen sadarwa na lardin Heilongjiang, kana ana kyautata zaton cewa hare-haren sun samu goyon-baya daga gwamnatin Amurka. Game da wannan batu, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya bayyana a jiya Alhamis cewa, rahoton ya sake nanata cewa, Sin babbar kasa ce a duniya dake jin radadin harin intanet a jikinta, inda ta bukaci Amurka da ta kara waiwayar abubuwan da ta yi, da dakatar da shafa wa sauran kasashe bakin fenti. Kazalika, kasar Sin za ta ci gaba da daukar duk wani matakin da ya wajaba don kiyaye tsaron intanet a gida.
Har wa yau, yayin ziyararsa yankin Caribbean kwanan nan, sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Antonio Rubio ya ce wai hanyar mota da kasar Sin ta shimfida a kasar Guyana ba ta da inganci sam, inda Amurka ta yi fatan samar mata da zabi na daban. Game da wannan batu, Guo Jiakun ya ce, ba kamfanin kasar Sin ne ya shimfida waccan hanyar mota ba, kuma tuni Guyana ta karyata labarin. Kasar Sin na ganin cewa, maimakon shafa wa kasar Sin bakin fenti, da rura wutar rikici, gara Amurka ta aikata wa sauran kasashe alheri na zahiri. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp