Leadership News Hausa:
2025-04-07@07:46:55 GMT

Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)

Published: 6th, April 2025 GMT

Yadda Amarya Za Ta Gyara Jikinta Har Zuwa Ranar Aure (II)

(3).sinadare gyaran jiki: to anan fa matsalar take don gaskiya awannan yanayin idan har kina so ki ga kyakkyawan sakamako dole sai kinsha supplement na gyaran jiki masu ciko da mace saboda anfison aga amarya acike baza ki gane dagaske nake ba sai kin zauna nan awaje namiji yagama tsaraki yana ce miki kin hadu kina jin kanki kawai sai ranar daran farko za ki fara ganin canji.

Saboda haka koda bayanshi ma akwai wasu supplement dazasu kara miki kyau lokacin aurenki yakamata kinemo asalin original kisha domin yawancin mata dakike ganin jikinsu sumul sumul kamar su sukayi kansu ki gansu kamar alashe yanzu duk su suke sha shikuma gaskiya beda wata matsala da yawa domin suna kokari wurin inganta shi sosai.

Zamu ci gaba mako mai zuwa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Amarya

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Benuwe, ta ceto fasinjoji 14 da wasu ’yan bindiga suka sace yayin da suke tafiya a kan hanyar Makurdi zuwa Otukpo.

Sai dai uku daga cikin fasinjojin sun rasu, ciki har da direban motar.

Sabon harajin Trump zai jefa tattalin arziƙin duniya cikin matsala — WTO Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin Kano

A cewar sanarwar da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, CSP Catherine Anene, ta fitar a ranar Juma’a, lamarin ya faru ne a ranar 3 ga watan Afrilu, 2025.

Wasu ’yan bindiga sun farmaki motar a yankin Otukpo Burnt Bricks, inda suka buɗe wa direban da wani fasinja da ke gaba wuta, lamarin da ya tilasta direban tsayawa.

’Yan sanda tare da jami’an tsaro sun isa wajen da abin ya faru cikin gaggawa.

Sun iske direban da wani fasinja a cikin mota kwance cikin jini, amma an garzaya da su asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsu.

’Yan bindigar sun yi awon gaba da sauran fasinjojin zuwa cikin daji.

A ranar 4 ga watan Afrilu, ’yan sanda sun bi sahunsu zuwa cikin dajin inda suka yi musayar wuta, wanda hakan ya sa suke tsere suka bar mutanen da suka sace.

Biyu daga cikin waɗanda aka sace an yi musu rauni da adda kafin a ceto su.

An samu nasarar ceto mutum 14, amma ɗaya daga cikinsu ya rasu a asibiti, sauran kuma suna karɓar magani.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Steve Yabanet, ya jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu, kuma ya sha alwashin kamo maharan.

Ya kuma buƙaci al’ummar Otukpo da su kai rahoton duk wanda suka gani da raunin harbin bindiga, domin an jikkata wasu daga cikin ’yan bindigar yayin artabu da jami’an tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arzikin Nijeriya Ya Habaka Zuwa Naira Tiriliyan 22.61 A Zangon Karshe Na 2024 – CBN
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • De Bruyne zai yi bankwana da Manchester City a ƙarshen kaka
  • Tsohon Gwamnan Oyo Olunloyo ya riga mu gidan gaskiya
  • An ceto fasinjoji 14 a hannun ’yan bindiga, 3 sun rasu a Benuwe
  • Adadin mutanen da suka mutu a girgizar kasa a Myanmar ya karu zuwa 3,354
  •  Falasdinawa 86 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata
  • Yadda aka yi jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi a Bauchi
  • Yadda yi jana’izar Dokta Idris Dutsen Tanshi a Bauchi