HausaTv:
2025-04-27@16:20:17 GMT

Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito

Published: 6th, April 2025 GMT

Gwamnatin kasar Sin ta yi kakkausar suka da bayyana adawarta ga matakin Amurka na kakaba “harajin fito na ramuwar gayya.”

A cikin wata sanarwar da ta fitar, ta yi Allah-wadai da matakin na Amurka, wanda ya kasance daukar mataki bisa radin kai, da kuma kariyar cinikayya da cin zarafin tattalin arziki.

Sanarwar ta kara da cewa, ta hanyar fakewa da abin da take kira “ramuwar gayya” da “adalci,” a zahiri dai Amurka ta tsunduma a aiwatar da dabarun danniya da babakere, tana neman cimma manufarta ta “Amurka na gaba da komai” da kuma “Amurka ta fi kowace kasa.” Har ila yau, Amurka na amfani da harajin fito don kawo cikas ga tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa, tare da fifita muradun Amurka sama da moriyar bai daya ta duniya, tare kuma da sadaukar da halaltattun muradun kasashen duniya don cimma burin Amurka.

A ranar Laraba ne dai shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da wani sabon tsarin haraji, inda ya sanya mafi kankantar harajin fito kashi 10 cikin dari kan kayayyakin da ake shigowa da su daga dukkan kasashe abokan huldar cinikayyarta da kuma karin sama da hakan kan waasu kasashen. Bayan matakin na Amurka, a ranar Juma’a kasar Sin ta sanar da cewa, za ta sanya karin harajin fito kashi 34 cikin dari kan dukkan kayayyakin da ake shigowo da su daga Amurka daga ranar 10 ga watan Afrilu, wanda ya yi daidai da harajin fito na ramuwar gayya da Amurka ta kakaba kan kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin.

A cikin sanarwar da gwamnatin kasar Sin ta fitar yau Asabar ta ce, kasar Sin ta dauki kuma za ta ci gaba da daukar kwararan matakai don kiyaye ‘yancinta, da tsaro, da muradunta na samun ci gaba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Sin ta harajin fito

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya

Li ya kara da cewa, Sin da Rasha sun bayyana goyon baya ga Iran wajen karfafa tattaunawa da hadin gwiwa da hukumar IAEA. (Mohammed Yahaya)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Za A Gudanar Da Zaben Sabon Paparoma Da Zai Gaji ‘Pope Francis’
  • Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Lashe Rayukan Mutane A Kudancin Iran
  • Gwamnan Babban Bankin Sin: Harajin Amurka Ya Jefa Kasuwanni Da Kasashe Masu Tasowa Cikin Hadari
  • Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
  • ‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara
  • A Karon Farko A Tarihi Adadin Lantarki Da Sin Ke Iya Samarwa Ta Karfin Iska Da Hasken Rana Ya Zarce Wanda Ake Iya Samarwa Ta Amfani Da Dumi
  • Kasar Sin Ta Goyi Bayan Rawar Da Hukumar IAEA Ke Takawa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran Ta Hanyar Diflomasiyya
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Amurka Ta Fara Dandana Kudar Manufar Kakaba Harajin Kwastam
  • Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam