Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
Published: 6th, April 2025 GMT
Jami’an tsaro sun jiran kayan ado na ’yan kunnayen zinare su wuce ta na’urar binciken fasinjan jirgin sama kafin a gano kayan da aka sace a hukumance.
An kama wani mutum mai shekara 32, mai suna Jaythan Lawrence Glider bisa zargin satar ’yan kunne biyu na zinare na sama da Dala Amurka 769,000 kwatankwacin Naira biliyan 1 da miliyan 177 dubu dari 615 da 840 daga wani babban kantin da ke Millenia a birnin Orlando da ke Jihar Florida a Amurka a ranar 26 ga Fabrairu.
A cewar sashen ’yan sanda na Orlando, Glider ya dauki matakin da ba a saba gani ba na haɗiye ’yan kunnayen da ya sace.
A cewar rahoton ’yan sanda da kafar yada labarai ta WFLA, Glider ya yi amfani da damar shiga sashen kayan ado masu tsada a kantin Tiffany & Co a ranar 26 ga Fabrairu ta hanyar nuna matsayin wakilin ɗan wasan ƙwallon kwando na Orlando Magic.
Rahotanni sun ce wannan dabarar ta ba shi damar shiga cikin sashen manyan kayayyaki masu tsada, inda ya yi awon gaba da su.
An kai shi kurkuku bayan an tsayar da motarsa a kan hanyar Interstate 10 a gundumar Washington.
An kama shi ne bisa zargin kin amincewa da kama shi, baya ga wasu fitattun sammaci guda 48 da aka gano daga Colorado.
Al’amura sun zama abin mamaki lokacin da Glider ya tambayi ma’aikatan gidan yarin, “Shin za a tuhume ni da abin da na hadiye?”
Wannan shigar da bincike da aka yi ya kai ga duba jikin mutumin, inda aka gano wasu abubuwan da hadiya a cikinsa.
Hukumomin sun yi zargin cewa, waɗannan ’yan kunnayen da aka sace, waɗanda darajarsu ta kai Dalar Amurka 769,000 (kwatankwacin Naira biliyan 1 da miliyan 177 dubu dari 615 da 840), inda aka yi zargin Glider ya haɗiye.
Jami’an tsaro a yanzu suna jiran gano kayan ta hanyar na’urar bincike.
Kamar yadda aka sani, haɗiye ƙananan abubuwa kamar ’yan kunnaye bai fiya haifar da babbar illa ba.
A cewar ƙwararrun likitocin, idan abin ya gaza inci ɗaya ko kuma ƙasa da inci 2, to zai iya wucewa ta hanji ba tare da haifar da wata matsala ba.
Glider yana da tarihin matsalolin shari’a, inda aka ba shi sammaci guda 48 a Colorado musamman ma, an kuma tuhume shi da laifin yin fashi a wani kantin Tiffany & Co da ke Texas a cikin shekarar 2022.
Bayan kama shi a baya-bayan nan, Glider na fuskantar tuhumar babbar sata a matakin farko da fashi da abin rufe fuska.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara
A watan Janairu kawai, marigayi shugaban ‘yan fashin daji, Isuhu Yellow, ya sanya harajin naira miliyan 172.7 a kauyuka 25, ciki har da bukatar amfanin gona.
A misali, an kakaba wa kauyen Gijinzama harajin naira miliyan 8.5, Dakolo naira miliyan 5 da buhunan wake 20, da Kibari, Kunchin Kalgo naira miliyan 20, Sungawa naira miliyan 15, da Yalwa naira miliyan 2.7, da dai sauransu.
Ba da jimawa ba, wani shugaban ‘yan fashin dajin nan, Dogo Gide, ya bukaci a biya naira miliyan 100 daga wasu al’ummomi 23 da ke karamar hukumar Tsafe, lamarin da ya sa jama’a suka kauracewa gidajensu.
Al’ummomin da abin ya shafa sun hada da Kunchin-Kalgo da aka nemi naira miliyan 20 daga wajensu, Sungawa naira miliyan 15, Rakyabu naira miliyan 15, da Kwaren Mai-Saje naira miliyan 10.
A ranar Lahadi, 20 ga Afrilu, ‘yan bindiga sun sake neman naira miliyan 60 daga mazauna kauyen Dankurmi a karamar hukumar Maru.
Wani mazaunin kauyen Kwalfada a karamar hukumar Tsafe wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya tabbatar da cewa ‘yan garkuwa da mutanen sun kakaba wa rayuka da dama haraji a yankin.
Ya ce, miliyoyin naira ne masu garkuwan suka nema a hannun jama’a ko kuma su kawo musu farmaki.
Wani mazaunin kauyen Dan Jibga, Mai suna Muhammad Dogo, ya ce ‘yan fashin daji sun sanya harajin naira miliyan 10 ga al’ummar Gama Lafiya bayan kashe wasu mutum biyu a ranar Lahadi da Litinin.
Dogo ya ci gaba da cewa, sauran kauyukan da harajin ya shafa sun hada da Unguwar Tofa naira miliyan 26.6, Makera naira miliyan 15, Sungawa naira miliyan 20, Rakyabu naira miliyan 7, Yalwa naira miliyan 8, Kwarin Mai Saje naira miliyan 11, Langa-Langa, inda harajin ya kai tsakanin naira miliyan 20 zuwa naira miliyan 30.
Ya kara da cewa ‘yan fashin dajin sun kwace kauyukan Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga, da Bilbis.
Wani mazaunin garin Mara da ke karamar hukumar Maru, Malam Ibrahim Maru, ya koka da yadda matsalar ‘yan fashin dajin ke ta kara ta’azzara a yankin Maru a ‘yan kwanakin nan.
Ya ce, “Hanyar Talata Mafara zuwa garin Maru ta zama tarkon mutuwa ga matafiya da direbobin wanda sun daina amfani da hanyar bayan karfe 4 na yamma.
“Da zarar karfe 4 na yamma ya yi zai yi wuya a samu direban da ke son daukar fasinjoji daga Maru zuwa Talata Mafara, kwanan nan na yi tattaki daga Talata Mafara zuwa Maru domin ziyarar jaje, amma da isa Maru, sai aka ba mu shawarar mu koma.
“Wannan hanyar ba ta da tsaro, ‘yan bindiga sun ci gaba da ayyukansu, suna gudanar da ayyukansu ba dare ba rana, sun yi garkuwa da mutane da dama, ciki har da mata da yara, a kauyuka daban-daban, kuma suna sanya haraji a kan al’ummomi da dama.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp