Aminiya:
2025-04-27@22:41:31 GMT

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba

Published: 6th, April 2025 GMT

Dakarun Soji  Operation WHIRL STROKE (OPWS), sun kashe ’yan bindiga uku a Ƙaramar Hukumar Karim Lamido da ke Jihar Taraba, tare da lalata sansanoninsu da kuma ƙwato makamai.

Wannan harin ya faru ne ranar 5 ga watan Afrilu, kamar yadda kakakin rundunar, Olubodunde Oni, ya bayyana a wata sanarwa.

Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya Abin da ya sa ba ma cin naman Akuya — Fulani

A cewarsa, da sojoji suka isa yankin Chibi, sai ’yan bindigar suka fara tserewa.

Amma sojojin sun bi sahunsu, suka yi musayar wuta da su, har suka kashe uku daga cikinsu, sannan suka lalata maɓoyarsu tare da ƙwato makamai masu hatsarin gaske.

Sanarwar ta kuma ce sojojin sun daɗe suna sintiri a yankin Dutsen Zaki da Achalle, inda suka tarwatsa sansanonin wasu ƙarin ’yan bindiga a baya-bayan nan.

Rundunar ta ce tana ci gaba da aiki tuƙuru domin kawo ƙarshen ayyukan ’yan ta’adda a faɗin Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Maɓoya Najeriya Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

An ‘Yi Mummunar Arangama Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato

 

Duk da haka, Mai Maciji ya bayyana cewa ‘yan bindigan sun gudu lokacin da matasan gari suka afka musu. Sun kona wani shago a kasuwar, amma wutar ba ta bazu zuwa sauran shaguna ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  • An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • An ‘Yi Mummunar Arangama Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • ‘Yansanda Sun Ƙwato Bindigogi Da Tabar Wiwi A Zamfara Bayan Artabu Da ‘Yan Bindiga
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa
  • 2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed
  • ’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa