Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan cewa ta ware kudade don gina kananan cibiyoyin kiwon lafiya a duk fadin kasar.

Jaridar daily Trust ta Najeriya ta nakalto mataimakin shugaban kasa Alhaji Shetima yana fadar haka a ranar Asabar a lokacinda yake kaddamar da cibiyar yaki da cutar daga a cikin asbitin koyon aikin likitanci ta OOUTH dage birnin shagamu na jihar Oyo.

Mataimakin shugaban kasar ya kara da cewa shirin gina wadannan kananan cibiyoyin kiwon lafiya dai yana daga cikin babban shirin gwamnatin mai ci na kyautata cibiyoyin kiwon lafiya a kasar gaba daya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci

Ƙungiyar Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF), ta yi Allah-wadai da harin da aka kai wasu ƙauyuka na Ƙaramar Hukumar Bokkos da ke Jihar Filato.

Ƙauyukan da abin ya shafa sun haɗa da Ruwi, Manguna, Daffo, Josho da Hurti.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba Fasinja ya yi ƙoƙarin buɗe ƙofar jirgi a sararin samaniya

Shugaban ƙungiyar kuma gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana waɗannan hare-hare a matsayin rashin hankali da tausayi.

Ya ce an kashe mutane da dama ciki har da mata da yara, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Ya ƙara da cewa irin waɗannan hare-hare na barazana ga zaman lafiya da haɗin kan yankin Arewa.

A wata sanarwa da kakakinsa, Ismaila Uba Misilli, ya fitar a Gombe, Gwamna Yahaya ya bayyana jimaminsa game da wannan mummunan lamari.

Ya jajanta wa iyalan waɗanda abin ya shafa da kuma gwamnatin Jihar Filato da al’ummarta baki ɗaya.

Gwamnan ya bayyana damuwarsa kan yadda rikici ke ci gaba da addabar yankunan karkara, musamman yadda ake yawan zubar da jinin bayin Allah.

“Rayuwar ɗan Adam abu ce girma da ba za a yi wasa da ita ba. Waɗannan mugayen hare-hare da ake kai wa mutane abin Allah-wadai ne, kuma dole ne a dakatar da su,” in ji Gwamna Yahaya.

Ya yaba da matakin gaggawa da Gwamna Caleb Mutfwang na Jihar Filato, ya ɗauka bayan faruwar lamarin, da kuma ƙoƙarin jami’an tsaro wajen shawo kan rikicin.

Sai dai ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara himma wajen kamo waɗanda suka aikata wannan aika-aika tare da tabbatar da cewa an hukunta su.

Gwamna Yahaya ya kuma buƙaci a ƙara ƙoƙarin wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, haƙuri da fahimtar juna a tsakanin al’umma, musamman tsakanin manoma da makiyaya.

Ya jaddada ƙudirin gwamnonin Arewa na aiki tare wajen kawo ƙarshen rikice-rikice, ta hanyar ƙarfafa tsaro, tattaunawa da aiwatar da manufofin da za su kawo zaman lafiya da haɗin kai.

Ya kuma buƙaci shugabannin al’umma, ƙungiyoyin addinai da na fararen hula da su tallafa wa gwamnati ta hanyar yaɗa sakon zaman lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An sayar da kare mafi tsada a duniya
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci
  • Afrika Ta Tsakiya: MDD Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Kiyaye Zaman Lafiya
  • Sharhi Kan Dabarun Kiwon Bijimin Sa
  • An Kaddamar Da Kwamitin Zaman Lafiya A Kananan Hukumomin Jahun Da Miga Na Jihar Jigawa
  • Manyan Cibiyoyin Kudi Na Duniya Sun Yi Gargadai Akan Sabbin Kudaden Fito Na Amurka
  • Saboda Rikicin Kasar Sudan Ta Kudu Shugaba Musaveni Ya Isa Birnin Juba
  •  Falasdinawa 86 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata