Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Kananan Cibiyoyin Kiwon Lafiya 8,880 A Duka Fadin Kasar
Published: 6th, April 2025 GMT
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwan cewa ta ware kudade don gina kananan cibiyoyin kiwon lafiya a duk fadin kasar.
Jaridar daily Trust ta Najeriya ta nakalto mataimakin shugaban kasa Alhaji Shetima yana fadar haka a ranar Asabar a lokacinda yake kaddamar da cibiyar yaki da cutar daga a cikin asbitin koyon aikin likitanci ta OOUTH dage birnin shagamu na jihar Oyo.
Mataimakin shugaban kasar ya kara da cewa shirin gina wadannan kananan cibiyoyin kiwon lafiya dai yana daga cikin babban shirin gwamnatin mai ci na kyautata cibiyoyin kiwon lafiya a kasar gaba daya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Nijeriya Na Kulla Yarjejeniya Da Kasar Sin Kan Noman Rake
Wannan dai, wani bangare ne na shirin kara habaka hada-hadar kawance tsakanin kasar da China.
Kazalika, hakan na daga cikin yunkurin Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Tinubu, na jawo masu zuba jari da yawansa ya kai kimanin dala biliyan daya a fannin habaka samar da Sikari a kasar.
Bisa tsarin wannan yarjejeniya, kamfanin zai kafa masana’antar Sikari da kuma gonar Rake da za su fara samar da tan 100,000 na Sikari a duk shekara.
Kazalika, Hukumar NSDC ita kuma, za ta taimaka wajen samar da duk takardu da kuma sahalewar gwamnati da ake bukata, domin fara aikin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp