Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya yada wasu hutunan bidiyo wanda yayi kama da na jiragen yakin kasar ne kan kasar Yemen, inda suka yi ruwan boma bomai a kan su a matsayin yan ta’ada wadanda suke shirin yakar Amurka, amma daya baya shaidu sun ta tabbatar da cewa taron ta yan kasar ta Yemen ne a birnin Hudaida wadanda suke bukin sallah karamar da ta gabata a ranar 4 ga watan Afrilun da muke ciki.

Labarin ya kara da cewa wannan aikin na sojojin Amurka ya na iya zama laifin yaki wanda ana iya gurfanar da gwamnatin Amurka kan laifukan yakin da ta ke aikatawa a yake-yakenta na kasashen waje.

Wannan zargin yana cewa ne bayan da sojojin Amurka suka fara kaiwa kasar Yemen hare-hare a cikin watan Maris da ya gabata, kuma ya zuwa yanzu sun kai mata hare-hare har fiye da 200.

Manufar gwamnatin kasar Amurka a yakin da take kaiwa kasar Yemen itace, raunan kasar ta Yemen a hare-haren da take kaiwa HKI, da kuma harba makamai kan jiragen ruwan kasuwanci na HKI wadanda suke wucewa ta tekub red sea.

A wani sakon X daga kasar Yemen da wani a Yemen ya mayarwa Trump. Y ace masa. Taron wata kabila ce daga kabilun lardin Hudaida, kuma ka kasa yin kome da kasar Yemen sai ka koma kashe fararen hula wadanda ba ruwansu da jiragen ku.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC

Hukumar Yaƙi Da Cututtuka Masu Yaɗuwa a Nijeriya, NCDC ta ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon cutar sanƙarau a Nijeriya ya kai 151.

Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna ƙaruwar waɗanda suka kamu da cutar daga 74 zuwa 156 a jihohin ƙasar 23.

Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back

Jihohin da aka fi samun yawan mace-macen sun haɗa da Kebbi, da Sakkwato da Katsina da Jigawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Borno da Kano da Adamawa da kuma Oyo.

NCDC ta ce ta tabbatar da kamuwar wasu mutum 126 daga cikin mutum 1,858 da aka yi zargin suna dauke da cutar a jihohin ƙasar 23.

Wani rahoto da NCDC ta fitar a ranar Lahadi, ta ce jihohin Jigawa, Yobe, Gombe, Katsina, Adamawa, Kebbi da kuma Sakkwato su ne sahun gaba na masu fama da cutar a bayan nan.

Cutar Sanƙarau dai cuta ce da aka fi ɗauka galibi a lokacin zafi.

Wasu mutanen na iya yaɗa cutar ba tare da sun san suna ɗauke da ita ba, akasarin mutanen da ke ɗauke da ita ba su sani ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta kaddamar da sabbin hare-hare kan Yemen
  • Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC
  • JMI Ta Kaddamarda Sabbin Ci Gaban Da Ta Samu Da Fasahar Nukliya A Ranar Makamashin Nukliya Ta Kasar
  • Faifan bidiyo ya fallasa kisan gillar da Isra’ila ta yi wa likitoci  a Gaza
  • Finafinan Kannywood da suke tashe da kuma manyan marubutansu
  • Francesca Albanze: Abinda Yake Faruwa A Gaza Kisan Kiyashi Ne
  • Al-Houthi: Hare-haren Amurka sun kasa dakatar da gwagwarmayar Yeman
  •  Falasdinawa 86 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata
  • Kasar Sin Na Nuna Damuwa Sosai Kan Harin Intanet Da Aka Kai Mata