Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
Published: 6th, April 2025 GMT
Rafael Grossi shugaban hukumar makamashin nukliya ta duniya (IAEA) ya bayyana cewa JMI bata da makamin Nukliya, sai dai tana dukkan kayan aikin da ake bukata, da kuma fasahar kera makamin idan tana bukatar yin hakan.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Grossi yana fadar haka a wata hira da yayi da tashar talabijin ta Agentina a yan kwanakin da suka gabata.
Abinda tambaya a nan itace tunda hukumar ta tabbatar da cewa a halin yanzu Iran bata da makaman Nukliya me yasa Amurka take tada hankali kuma take barazana ga kasar dangane da shirin ta na makamashin Nukliya al-hali bata da shi?
Grossi ya bayyana cewa al-amuran siyasa da kuma takurawa kasar da kasashen yamma suke yi shi ne yake ruruta rikicin da ke faruwa tsakanin Iran da kasashen yamma. Shugaban ya tabbatar da cewa gwamnatin JMI tana bada hadin kai ga masu binciken hukumar wadanda suke gudanar da bincike a dukkan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar ta Iran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : kasashen turai sun tafka kure na tarihi, ta hanyar goyan bayan Isra’ila
Iran ta bakin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, Esmail Baghai, ta ce nahiyar turai sun tafka kure na tarihi, ta hanyar goyon bayan Isra’ila ta hanyar yin watsi da sammacin kama Benjamin Netanyahu.
Esmail Baghai ya bayyana haka ne a cikin wani sako a asusunsa na X, bayan ziyarar aiki da Netanyahu ya kai kasar Hungary duk da sammacin kame shi da kotun ICC ta bayar kan laifukan yaki da cin zarafin bil adama da gwamnatinsa ta yi a zirin Gaza.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya ce : Sammacin kame jami’an gwamnatin Isra’ila da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta yi na nuni da yadda duniya ke nuna bacin rai kan kisan kiyashi, laifukan yaki, da laifukan cin zarafin bil’adama a Gaza, da kuma babbar bukatar kiyaye dokokin kasa da kasa da kuma kawo karshen rashin hukunta masu aikata munanan laifuka kan Falasdinawa.
A yammacin ranar Laraba ne Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya sauka a Budapest domin gudanar da ziyarar kwanaki hudu bisa gayyatar firaministan kasar Hungary Viktor Orban.
Shugaban masu tsattsauran ra’ayi na kasar Hungary ya gayyaci takwaransa na Isra’ila duk da cewa ana zargin Netanyahu da amfani da yunwa a matsayin hanyar yaki da kuma aikata laifukan cin zarafin bil’adama da suka hada da halaka a lokacin yakin kare dangi a Gaza.
A matsayinsa na mamba a kotun ICC, ya kamata kasar Hungary ta kama Netanyahu da ya isa kasar ta tsakiyar Turai tare da mika shi ga kotu, amma haka ya bar kasar salin alin.
Kotun ICC ta yi Allah wadai da Hungary saboda kin bin sammacin kama Netanyahu.