An gudanar da taro na farko na kwamitin raya cinikayya da kiyaye muhalli na hukumar kula da cinikayya ta duniya wato WTO na shekarar 2025 a birnin Geneva dake kasar Switzerland a kwanakin baya, inda tawagar wakilan kasar Sin ta karbi bakuncin taron tattaunawa kan hadin gwiwar fasaha da cinikayya da sana’o’i masu kiyaye muhalli, inda aka gabatar da dabarun Sin na raya sana’o’i da fasaha masu kiyaye muhalli.

A cikin jawabansu, masanan Sin sun yi amfani da ayyukan samar da makamashin da ake iya sake amfani da su, a kasashen Habasha da Sri Lanka da kuma aikin daidaita matsalar wutar lantarki na Afirka da sauransu a matsayin misalan dabarun Sin na hadin gwiwar fasaha. Fasahohin Sin sun kunshi fannnoni uku, na farko shi ne muhimmancin tsara shiri da yin hadin gwiwa, wato kasar Sin ta tsara shirye-shirye da tsarin hadin gwiwa don taimakawa sauran kasashe wajen gudanar da ayyukan yau da kullum na raya fasaha da yanayin aiwatar da shirye-shiryen. Na biyu shi ne aikin da aka gudanar bisa halin da ake ciki, wato kasar Sin ta kiyaye kyautata hadin gwiwar fasaha bisa bukatun wurin don tabbatar da yin amfani da fasahar wajen biyan bukatun raya wurin yadda ya kamata. Na uku shi ne horaswa da gabatar da fasahohi, wato kasar Sin ba ma kawai samar da na’urorin fasaha take yi ba, har da horar da kwararru da ba da ilmi don inganta karfin kwararrun wurin a wannan fanni. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka

Wasu masana a tarayyar Najeriya sun jinjinawa yadda Najeriya da Sin suka daga dangantakarsu zuwa huldar abota bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni a bara, matakin da ya tabbatar da goyon bayansu ga kokarin tinkarar kalubalen karin harajin kwastam da Amurka ke dora musu bisa radin kai.

Kwanan baya, an gudanar da taron tattaunawa kan yadda za a tinkari harajin kwastam da Amurka ke kakabawa sauran kasashe a birnin Abuja hedkwatar Najeriya, inda babban darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin ta Najeriya Charles Onunaiju ya bayyana cewa, hadin gwiwar Sin da Najeriya bisa dandalin tattauna hadin kan Sin da Afirka, da shawarar “ziri daya da hanya daya” da dai sauransu, ba ingiza bunkasuwar manyan ababen more rayuwa a Afirka kadai ya yi ba, har ma ya inganta karfin Najeriya da sauran kasashen Afrika, na tinkarar kalubaloli, da barazanar da Amurka ke haifarwa duniya.

Baya ga hakan, darektan cibiyar nazarin huldar Sin da Afrika a sabon zamani a jami’ar Abuja Sheriff Ghali Ibrahim, ya ce, kasuwar Afirka na da cikakken boyayyen karfi, kuma duba da yawan al’ummar Najeriya, tana da muhimmanci matuka ga tattalin arzikin Afirka, don haka sabuwar huldar da Najeriya da Sin ke kullawa, za ta yi babban tasiri ga kyautatuwar tsarin ciniki na duniya.

Dadin dadawa, babban manajan kungiyar hadin gwiwar manoman Najeriya wato NFGCS Retson Tedheke ya ce, dabaru da basirar bunkasar kasar Sin abubuwan koyi ne masu daraja ga nahiyar Afirka, kuma za su taka rawa wajen tinkarar kalubaloli bisa hadin kai. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 
  • Hakar man Kolmani: Jihohin Bauchi da Gombe sun gana da NNPC kan bukatun al’umma
  • An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing
  • Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba
  • Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai
  • Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka
  • Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
  • An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Salon “Kasa Daya Manufa Daya” Ya Dace Da “Ayyuka Goma” Na Hadin Gwiwa Da Afirka