Aminiya:
2025-04-07@13:58:31 GMT

ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato

Published: 7th, April 2025 GMT

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa wajen kawo ƙarshen hare-haren da ake kai wa al’umma a Jihar Filato.

Ƙungiyar ta bayyana baƙin cikinta matuƙa kan harin da aka kai yankin Bokkos da Mangu a ranar 28 ga watan Maris, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama ciki har da ƙananan yara.

’Yan sanda sun soke gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, Farfesa T.A. Muhammad-Baba ya fitar, ACF ta yi tir da waɗannan hare-hare tare da miƙa sakon ta’aziyyarta ga iyalan waɗanda suka rasu da kuma ɗaukacin jama’ar Jihar Filato.

Ƙungiyar ta ce hare-haren na ƙara jefa yankin Arewa cikin mawuyacin hali na rashin tsaro.

ACF ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ayyana dokar ta-ɓaci a wuraren da ake fama da hare-haren ‘yan bindiga tare da haɗa kai da al’ummomin yankin domin daƙile barazanar tsaro.

Haka kuma, ƙungiyar ta nemi gwamnati ta ƙara ƙaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma kama waɗanda ke da hannu a ta’asar.

Ƙungiyar ta jaddada buƙatar wanzar da zaman lafiya a Jihar Filato tare da buƙatar a haɗa kai da shugabannin gargajiya, dattawa, ƙungiyoyi da sauran masu ruwa da tsaki domin daƙile lamarin.

ACF ta kuma bukaci al’umma su riƙa bai wa jami’an tsaro bayanai kan duk wani abu da ka iya kawo matsala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa Gwamnatin tarayya hare hare kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili

Tsohon Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Kano kuma tsohon Mashawarci na Musamman ga Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya, CP Muhammad Wakili (ritaya), ya jaddada cewa dole ne ’yan sanda su yi amfani da ikon da suke da shi cikin gaskiya da adalci, don tabbatar da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Da yake jawabi a wani taron tattaunawa da masu ruwa da tsaki a Gombe, a matsayin wani ɓangare na bikin makon ’yan sanda, CP Wakili ya ce ba zai yiwu jami’an tsaro su gudanar da ayyukansu yadda ya kamata ba tare da goyon bayan al’umma ba.

An ceto yara ’yan Taraba da aka yi safararsu zuwa Kudu Adadin waɗanda suka mutu a harin Filato ya kai 52

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su kasance ƙofar su a buɗe ga jama’a, su saurari ƙorafe-ƙorafensu, tare da gina kyakkyawar alaƙa da su.

” ’Yan sanda ba abokan gaba ba ne ga jama’a, su ne ginshiƙin tsaro da ci gaba. Amma dole ne su kula da yadda suke amfani da ikon da aka ba su, domin kada ya rikiɗe ya zama cin zarafi,” in ji Wakili.

Ya yabawa Kwamishinan ’Yan sanda na Jihar Gombe, CP Bello Yahaya, bisa ƙwazon da yake nunawa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Wakili ya kuma buƙaci al’umma da su bada haɗin kai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya a Gombe da ƙasa baki ɗaya.

A nasa jawabin, Kwamishinan ‘Yan sanda na Gombe, CP Bello Yahaya, ya jaddada cewa Ranar ‘Yan Sanda ta Duniya, da ake gudanarwa duk shekara na da nufin tunawa da irin rawar da ’yan sanda ke takawa wajen tabbatar da tsaro.

Ya buƙaci jami’an ’yan sanda da su ƙara ƙaimi wajen kusantar da kansu ga jama’a, su nuna gaskiya da ƙwarewa a ayyukansu, domin gina amana da fahimtar juna.

A nasa ɓangaren, Kwamishinan Harkokin Tsaro da Cikin Gida na Gombe, Laftanar Kanar Abdullahi Bello (ritaya), ya jinjinawa CP Yahaya bisa shirya wannan muhimmin taro.

“Wannan irin shiri yana taimakawa wajen gina kyakkyawar fahimta tsakanin jami’an tsaro da jama’a. Ina kira ga rundunar ’yan sanda da su ci gaba da irin waɗannan shirye-shirye,” in ji shi.

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana cewa manufar wannan bikin ita ce kusantar da jama’a ga ’yan sanda tare da inganta ayyukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 
  • Hassan Fadlallah: Amurka ke da alhakin ayyukan wuce gona da iri na Isr’aila a Lebanon
  • ACF Ta Bukaci Gwamnatin Najeriya Da Ta Kawo Karshe Tashe-Tashen Hankula Filato
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci
  • Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
  • Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang
  • ’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili
  • Adadin waɗanda suka mutu a harin Filato ya kai 52
  • Dalilan Da Suka Sa Gwamnatin Tarayya Zamanantar Da Wuraren Kiwo 417