Kicibus: An Gabza Yaki Tsakanin Yan Bijilanti Da ‘Yan Fashi, Sun Kashe Barayi 30 A Zamfara
Published: 7th, April 2025 GMT
Aƙalla mutane 30 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne, sun mutu a wani mummunan hari da kungiyar ‘yan sa kai ta cikin gari ta yi a yankin Dansadau na karamar hukumar Maru, jihar Zamfara.
Kamar yadda wani masani kan yaki da ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana daga bayanan sirri, harin ya faru ne a kimanin karfe 2 na rana a ranar Alhamis, 4 ga Afrilu.
An ce ‘yan fashin suna kan hanyarsu ta kai hari wani kauye kusa da su, amma sai suka yi kicibus da ‘yan sa kai na yankin, Yansakai, wadanda suka mamaye wajen shahararren birnin. A cikin artabun da ya biyo baya, an samu mutuwar waɗanda ake zargin su da kai hare-hare.
Haka kuma, an samu motocin haya guda 16 da ake zargin ‘yan fashin sun yi amfani da su yayin kai hare-haren, kamar yadda Makama ya shaida.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Jiragen Yakin Amurka Sun Kai Sabbin Hare Hare Kan Yakuna 4 A Kasar Yamen
A cikin sabban hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Yemen a jiya Alhamis sun kai hare-hare kan larduna guda 4 .
Tashar talabijin ta Presstva anan Tehran ta nakalto majiyar labarai daga kasar ta Yemen jiragen yakin Amurka suna kai hare-haren a kan kasar kusan ko wani rana.
Amurka dai tace tana kai wadan nan hare-hare kan kasar Yemen ne sai ta dakadar da kaiwa HKI hare-hare don goyon bayan Falasdinawa a Gaza, sannan ta dakatar da kaiwa Jiragen HKI da kuma na Amurka hare-hare a cikin tekun maliya.
Kamfanin dillancin labaran SABA NEWS na kasar Yemen ya nakalto wani jami’an gwamnatin kasar wanda bai son a bayyana sunansa yana cewa jiragen yakin Amurka sun kai hare hare a safiyar yau Jumma’a a tsibirin Kamaran da ke kudancin kasar kusa ba bakin tekn red sea.
Sannan makaman na Amurka sun fada kan yankin Bani Hushaysh da ke daya daga cikin lardunan da suke kusa da San’aa babban birnin kasar.
Labaran sun kara da cewa makaman Amurka sun fada kan garin Hakamal-Haymah da yankin Manakhah duk a kusa da birnin san’aa.