Aminiya:
2025-04-27@22:48:49 GMT

’Yan sanda sun janye gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah

Published: 7th, April 2025 GMT

Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya janye gayyatar da aka yi wa Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, kan hawan sallah.

Maimaikon ya Sarkin ya je Abuja domin yi masa tambayoyi, Sufeto Janar ya umarci rundunar ’yan sandan jihar, yi wa Sanusi II tambayoyi.

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da hare-haren Filato, sun nemi a yi adalci Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Taraba

Kakakin ’yan sanda na ƙasa, Olumuyiwa Adejobi ne, ya bayyana hakan, inda ya ce an soke gayyatar ne bayan da wasu manyan mutane a ƙasar suka shiga lamarin.

Ya ƙara da cewa ’yan sanda na son kauce wa duk wani da zai danganta lamarin da siyasa ko wani abu daban.

Idan ba a manta ba hedikwatar ’yan sanda ta ƙasa ce, ta gayyaci Sarkin, domin ya bayar da bayani game da wani abin da ya faru a lokacin bikin Sallah a Kano.

Tun da farko, rundunar ’yan sandan jihar, ta dakatar da duk wasu hawan Sallah da suka haɗa da jerin gwanon dawakai, saboda matsalar tsaro.

Amma a ranar 30 ga watan Maris, yayin da Sarkin ke tafiya zuwa filin Idi na Ƙofar Mata domin Sallar Idi, an kashe wani jami’in sa-kai da ke tsaronsa ta hanyar caka masa wuƙa, sannan wasu kuma sun jikkata.

Bayan haka, wasu majiya sun ce Sufeto Janar na ’yan sanda, Kayode Egbetokun, ne, ya umarci Kwamishinan ’yan sandan jihar da ya kama Sanusi II.

Sai dai Kwamishinan ya shaida masa cewa abin da ya faru bai shafi karya dokar hana hawan Sallah ba, kuma Sarkin bai hau doki ba wajen ziyarar gidan gwamnati kamar yadda ake yi a da.

Sai dai duk haka Sufeton ya umarci sashen leƙen asiri na ’yan sanda da su gayyaci Sarkin zuwa Abuja domin amsa tambayoyi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Hawan Sallah Sufeto Janar Na Yan Sanda Tambayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

A wata hira da Jammaje ya yi da rfI Hausa an jiyo shi ya na cewa sunana Kabiru Musa Jammaje haifaffen Jihar Kano, nayi karatu a Bayero Unibersity da ke birnin Kano inda na karanci English kafin in tafi kasar Amurka domin zurfafa karatu, bayan na dawo gida Nijeriya kuma na shiga Jami’ar koyo daga gida ta NOUN inda na karanci ‘Education Administration and Planning’.

 

Jammaje ya ci gaba da cewa a yawace yawacen da na yi na tafi kasashe irinsu Afirika Ta Kudu da kasar Kenya inda a wancan lokacin sai na lura cewa mutanen wadannan kasashen biyu suna yi wa duk wani dan Nijeriya wani kallo na daban sakamakon abin da suka ga ana nunawa a wasu fina finan da suke kallo da ake shiryawa a kudancin Nijeriya (Nollywood, ganin ana nuna abubuwa kamar tsafe-tsafe, fashi da makami, damfara ko kuma mutane masu shan jini.

 

Hakan yasa suke yi wa duk wani da ya zo daga Nijeriya irin wannan kallon, wannan sai ya ja hankalina na ce to mi zai hana mu da muke yin fina-finai da babu duk wadannan abubuwa marasa kyau a cikinsu a nan Arewacin Nijeriya (Kannywood) mu kawo masu namu fina-finan su kalla, sai kuma naga cewar babu wata hanya da hakan za ta iya faruwa sai idan wadannan mutane za su ji abin da muke fadi a fina-finan.

 

Wannan ne ya kara mani kwarin gwuiwar tunkarar wannan aiki gadan-gadan, sai na tuntubi wasu daga cikin abokaina da ke a masana’antar kamar su Falalu Dorayi, Abba El Mustapha da sauransu domin zakulo hanyoyin da za su kaimu ga samun nasara, kuma Alhamdulillahi hakan ya matukar tasiri domin kuwa abin da muke yi a yanzu ya samu karbuwa a ciki da wajen Nijeriya in ji Jammaje.

 

Jammaje wanda yanzu haka yake da makarantun koyar da harshen Turanci a mafi yawancin jihohin Arewacin Nijeriya ya ci gaba da cewa, a lokacin da na shigo masana’antar Kannywood ban yi tunanin bayan Ali Nuhu akwai wadanda suke jin turanci ba, amma kuma bayan na shiga sai na gano akwai wadanda su ka kware sosai a turanci a masana’antar wanda hakan sai ya sau kaka mana aikin.

 

Da yake amsa tambaya a kan wace irin nasara ya samu tun bayan fara wannan yunkurin Kabiru Musa Jammaje ya ce akwai tarin nasarori da aka samu, domin kuwa a shekarar 2017 a wata ziyara da ya kai kasar Ingila akwai wasu iyali da ya nuna masu fim din There Is A Way, sai suke mamaki har suna tambaya dama akwai wani yanki da ake kira Arewa a Nijeriya, sai suke cewa basu taba jin wani yare wai Hausa ba, sai na ce masu ai wannan fim fin kacokan dinsa an yi shi ne a arewacin Nijeriya kuma duka abin da suka gani shi ne asalin abin da bahaushe ya kunsa, kama daga zamantakewa, al’ada da kuma yanayin sutura sai suka dinga mamaki.

 

Sannan kuma fina finan da muka yi sun samu daukaka sosai don kuwa har da kyautuka muka dinga samu a ta sanadiyarsu kamar fim din ‘In Search Of The King’ da ya taba lashe kyautar Fim Mafi Kyawu a wani bikin karramawa da aka yi, sai kuma sabon fim dinmu mai suna Nanjala wanda yanzu haka akwai wani wurin yawon bude ido da ke kasar Turkey da suka saye fim din domin su nunawa bakinsu (Tourist) irin yadda al’adar mutanen kasashen Afirika musamman Arewacin Nijeriya ta ke.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • Sarkin Kano Na 15, Aminu Ado Bayero Zai Naɗa Ɗan Uwansa Sanusi Ado A Matsayin Galadiman Kano
  • Samarin Arewa sun yaba wa Sarkin Daura kan bai wa Ja’o’ji muƙami
  • Sarkin Daura Zai Karrama Ja’o’ji Da Wasu Samarin Arewa
  • Samarin Arewa sun yaba wa Sarkin Daura kan bai wa Ja’o’ji muƙami
  • Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa
  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe