An sayar da kare mafi tsada a duniya
Published: 7th, April 2025 GMT
Kwanan nan wani mai kiwon karnuka a Indiya ya biya Rupee miliyan 500 — kwatankwacin Naira biliyan 8 da miliyan 949 da dubu 481 da 589 domin sayen wani karen kerkeci na jinsin karen Shephard Caucasian, wanda hakan ya sa karen ya zama mafi tsada a duniya.
Karen mai suna Cadabomb Okami, an bayar da rahoton cewa, an yi kiwon karen mafi tsadar ne a Amurka kuma S.
Ya shahara saboda tarin nau’ukan karnuka sama da 150, ciki har da wasu da ba kasafai ba ake samun su a wasu sassan duniya.
Satish ya shaida wa manema labarai a Indiya cewa, yana jin cewa farashin Rupee miliyan 500 ya dace da Cadabomb Okami saboda a zahiri yana da nau’i na daban.
Bugu da ƙari, jinsi ne mai ban sha’awa, yana dan wata takwas kacal ya riga ya kai nauyin kilo 75 kuma tsayinsa ya kai inci 30.
“Shi wani jinsin kare ne da ba kasafai ba ake samun sa kuma yana kama da kerkeci. Wannan jinsin karen ba a taba sayar da shi a duniya a baya ba,” in ji S. Satish.
“Ina kashe kudi a kan wadannan karnuka saboda ba su da yawa. Ban da haka, ina samun isassun kuɗi domin a koyaushe mutane suna sha’awar ganin su, suna daukar hoton salfi na hotuna.
“Ni da karena mun fi samun kulawa fiye da ɗan wasan kwaikwayo a wurin kallon fim! Mu duka biyun masu jan hankali ne.”
Abin sha’awa, wannan ba shi ne farkon siyayyar karen Indiyawan da mai kiwon karnukan ya saya mai tsada ba.
A bara, ya sayi wani kare jinsin ChowChow, wanda ba kasafai ake samun baye irinsa ba, wanda ake zargin yana da kamanceceniya da dabbar dawa ta ‘red panda’ a kan Dala miliyan 3.25 — kwatankwacin Naira biliyan 4 da miliyan dari 964 da dubu dari 3 da dubu 75.
Satish yana kiwon karnukansa sama da 150 a filin kadada bakwai kuma yana nuna jinsinsu a tarukan da ke faruwa a Indiya, inda ake biyan sa tsakanin Dala 3,000 kwatankwacin Naira miliyan 4 dubu dari 5 da 82 da dubu 2500.
Ya riga ya fara amfani da Okami don dawo da jarinsa, inda yake nuna shi a wasu manyan taruka da aka yi, ciki har da shirin farkon buɗe sababbin finafinai, a Karnataka.
Ya yi iƙirarin cewa, mutane suna ta yin tururuwa don ganin kare mafi tsada a duniya fiye da yadda suka saba gani a sauran karnukan nasa.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Malaman Musulunci Ta Duniya Ta Yi Fatawar Wajabcin Taimakawa Falasdinawa
A wata sanarwa da kungiyar ta malaman addinin musulunci ta duniya ta ce wajibi ne akan kowane musulmi wanda yake da iko a fadin duniyar musulunci da ya taimakawa mutanen Gaza da makamai da kayan yaki domin dakile ta’addancin Isra’ila da yake cigaba.
A jiya Juma’a ne kungiyar malaman addinin musuluncin ta duniya ta fitar da wannan fatawa wacce ta kunshi yin kira ga daidaikun musulmi da kuma gwamnatocinsu da su bai wa kungiyoyin gwgawarmaya makamai da kayan yaki da kuma bayanai na sirri akan abokan gaba.
An gina fatawar ne akan cewa matakin farko na wajabcin jihadin akan al’ummar Falasdinu, sannan kasashen dake makwabtaka da Falasdinu da su ka hada Masar, Jordan da kuma Lebanon, sannan kuma dukkanin kasashen larabawa da musulmi.
Har ila yau Fatawar ta yi kira ga musulmin da su yunkura cikin hanzari ba tare da ba ta lokaci ba ta fuskokin soja, tattalin arziki da kuma siyasa.
Sanarwar ta kuma ce, bayan kashe mutane fiye da 50,000 babu makawa a dakatar da wannan kisan kiyashi da kuma barna mai girma da take faruwa.
Kungiyar malaman musulmin duniya ta kuma kira yi kasashen musulmi da suke da alaka da Isra’ila da su yanke ta.