Rahoto: Yara Falasdinawa 350 ne Isra’ila ke tsare da su a gidajen kurkuku
Published: 7th, April 2025 GMT
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, a yayin bikin ranar yara kanana ta duniya a Falasdinu, cibiyoyi masu fafutuka kan harkokin fursunoni sun sanar da cewa: Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila tana ci gaba da tsare kananan yara Palastinawa sama da 350 a gidajen yari da wuraren da ake tsare da fursunoni.
Sanarwar hadin gwiwa da hukumar kula da harkokin tsare-tsare, da “Kungiyar Fursunonin palasdinu”, da kuma “Cibiyar Kare Hakkokin Bil Adama ta Al-Dameer” suka fitar, ta bayyana cewa, yaran na fuskantar matsaloli Ciki har da azabtarwa, yunwa da gangan, da rashin kulawar likita.
Wadannan cibiyoyi sun jaddada cewa yaran Palasdinawa su ma suna fuskantar tauye hakkinsu, wanda irin wannan hali ne ya yi sanadin shahadar wani yaro a cikin makon nan a gidan yarin Isra’ila.
A cewar wadannan kungiyoyi, tsare yara bias irin wannan tsari na Isra’ila yana karuwa, kuma manufarsu ita ce kawar da yaran daga cikin iyalansu da lalata kuruciyarsu. Kuma wannan shi ne a lokacin da aka fi kai hare-hare mafi muni a tarihi kan yaran Palastinawa, yayin da ake ci gaba da kisan kiyashin, dubban yara ne suka yi shahada, wasu dubbai kuma suka jikkata ko kuma sun rasa iyalansu.
Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun kuma sanar da cewa, tun bayan da aka fara kisan kiyashin, an samu sauye-sauye a halin da ake ciki na fursunoni yara.
Game da yara a Gaza, saboda ci gaba da tilsta manufar korar jama’a daga yankunansu da Isra’ila ke aiwatarwa, yara da dama sun rabu da iyalansu.
Duk da tsauraran matakan hana kai ziyara, kungiyoyin lauyoyi sun yi nasarar ganawa da wasu daga cikin yaran da ake tsare da su a gidajen yarin Ofer, Megiddo, da Damon, kuma an tattara shedu da dama da suka nuna irin yadda ake azabtar da su da kuma tauye hakki akan wadannan yaran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al-Houthi: Hare-haren Amurka sun kasa dakatar da gwagwarmayar Yeman
Madugun kungiyar Ansarallah ta kasar Yeman ya yi ikirarin cewa, zafafan hare-haren wuce gona da iri da Amurka ke kaiwa kasar Yemen, ya kasa dakatar da ayyukan gwagwarmayar Yeman na goyon bayan al’ummar Gaza ko kuma kare jiragen Isra’ila a tekun Bahar Rum.
A wani jawabi da ya yi a ranar Juma’a, Abdul-Malik al-Houthi ya ce Amurka ta zafafa kai hare-hare a kan kasar Yemen, inda wasu lokutan ta kai hare-hare sama da 90 a kowace rana, a wani bangare na goyon bayan da take baiwa kasar Isra’ila a yakin kisan kare dangin da ta ke yi a zirin Gaza.
Duk da haka, ya jaddada cewa, hare-haren na Amurka “sun kasa dakatar da ayyukan soji da ke tallafawa al’ummar Falasdinu, ko kuma tabbatar da kare zirga-zirgar jiragen ruwa na Isra’ila a cikin Bahar Maliya, Gulf na Aden da kuma Tekun Oman.”
Ya kuma ce jami’an sojin Amurka sun amince cewa hare-haren sun kasa dakile karfin sojojin Yemen.
Al-Houthi ya ce: “Amurka ta gaza cimma burin da ta sanya a gaba na kawar da shugabanni da kuma kawar da ‘yantacciyar kasar Yemen.”
Ya yi alkawarin cewa kasar Yemen za ta ci gaba da kai hare-hare na daukar fansa, kafin ya bayyana cewa: “Amurka ba ta tsoratar da mu.”
Shugaban kungiyar Ansarallah ya kuma gargadi gwamnatocin kasashen Larabawa da kasashen da ke makwabtaka da su kan goyon bayan hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen sannan ya kara da cewa kutsawar da Ministan Isra’ila mai tsatsauran ra’ayi, Itamar Ben-Gvir ya yi a harabar masallacin Kudus, shaida ce ta ci gaba da cin zarafi da Isra’ila ke yi kan “daya daga cikin mafi girman wurare masu tsarki ga musulmi.”