Araqchi: Babu Wata Tattaunawa Da Aka Gudanar Tsakanin Amurka Da Iran
Published: 7th, April 2025 GMT
Iran ta sake nanata matsayinta na kin shiga shawarwari kai tsaye da Amurka kan shirinta na nukiliya, maimakon haka ta bukaci a ci gaba da shawarwarin ta hanyar masu shiga tsakani.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya bayyana hakan, yana mai cewa babu wata tattaunawa da aka da Washington, kuma ba za a yi irin wannan tattaunawa ba sai dai ta hanyar masu shiga tsakani.
“Mun bayyana matsayinmu, muna goyon bayan bin hanyoyi na diflomasiyya da tattaunawa, amma ta hanyar masu shiga tsakani. Tabbas, ba a gudanar da wata tattaunawa kai tsaye tsakanin Iran da Amurka ba, ” in ji Araghchi a cikin wata sanarwa da ya fitar a dandalin Telegram.
Kalaman nasa sun zo ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai wa Iran hari idan ta ki amincewa da kulla wata sabuwar yarjejeniya kan shirinta na nukiliya.
Araqchi yace, Iran ba zata taba yarda da duk wani mataki na shigo-shigo ba zurfi ba, domin kuwa irin wannan ne aka yi wa kasar Libya, a lokacin da ta yi watsa da shirinta na nukiliya kuma aka ci gaba da kakaba mata takunkumai, daga karshe kuma kasashen turai da kungiyar tsaro ta NATO suka hambarar da gwamnatin kasar a lokacin mulkin Ghaddafi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Pezeshkian ya soki barazanar Amurka kan kasarsa game da tattaunawar nukiliya
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya soki abunda ya danganta da barazanar Amurka ga Teheran, yana mai cewa kasarsa a shirye take ta shiga tattaunawa ta hakika ba tare da barazana ba.
“Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman tattaunawa ta gaskia, a yayin da suke barazana ga Iran a daya bangaren kuma suna neman yin shawarwari,” in ji Pezeshkian a ranar Asabar.
“Idan kuna neman shawarwari, to me yasa kuke yin barazana? A yau, Amurka ba wai kawai ta wulakanta Iran ba har ma da duniya, kuma wannan hali ya saba wa bukatar tattaunawa,” in ji shi.
Kalaman na Pezeshkian sun zo ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi kira ga Tehran da ta shioga shawarwari kai tsaye kan shirinta na nukiliya yayin da ya yi barazanar jefa bama-bamai a Iran idan diflomasiyya ta gaza.
A ranar Lahadin da ta gabata, ne Trump ya sake yi wa Iran barazanar kai harin bama-bamai da kuma lafta mata takunkumai masu tsauri a karo na biyu idan ba ta cimma matsaya da Washington ba kan shirinta na nukiliya, a yayin da kuma Amurka ta kara tura karin jiragen yaki zuwa yankin.
Tunda farko Ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araghchi ya sake nanata shirin Tehran na shiga shawarwarin da Amurka kan shirinta na nukiliya na zaman lafiya, saidai yana mai gargadin cewa barazanar Amurka na dagula halin da ake ciki.