Araqchi: Babu Wata Tattaunawa Da Aka Gudanar Tsakanin Amurka Da Iran
Published: 7th, April 2025 GMT
Iran ta sake nanata matsayinta na kin shiga shawarwari kai tsaye da Amurka kan shirinta na nukiliya, maimakon haka ta bukaci a ci gaba da shawarwarin ta hanyar masu shiga tsakani.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ya bayyana hakan, yana mai cewa babu wata tattaunawa da aka da Washington, kuma ba za a yi irin wannan tattaunawa ba sai dai ta hanyar masu shiga tsakani.
“Mun bayyana matsayinmu, muna goyon bayan bin hanyoyi na diflomasiyya da tattaunawa, amma ta hanyar masu shiga tsakani. Tabbas, ba a gudanar da wata tattaunawa kai tsaye tsakanin Iran da Amurka ba, ” in ji Araghchi a cikin wata sanarwa da ya fitar a dandalin Telegram.
Kalaman nasa sun zo ne bayan da shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai wa Iran hari idan ta ki amincewa da kulla wata sabuwar yarjejeniya kan shirinta na nukiliya.
Araqchi yace, Iran ba zata taba yarda da duk wani mataki na shigo-shigo ba zurfi ba, domin kuwa irin wannan ne aka yi wa kasar Libya, a lokacin da ta yi watsa da shirinta na nukiliya kuma aka ci gaba da kakaba mata takunkumai, daga karshe kuma kasashen turai da kungiyar tsaro ta NATO suka hambarar da gwamnatin kasar a lokacin mulkin Ghaddafi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe Shugaban coci da wata mace a Benuwe
A wani sabon tashin hankali ya yi sanadiyyar rasa rayukan wani shugaban cocin Roman Katolika da wata mata a ƙauyen Ayua da ke gundumar Mbayer/Yandev a ƙaramar hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Shedun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne a daren ranar Talata, lamarin da ya sa mazauna yankin da ke kewayen yankin Mbagwen da ke ƙaramar hukumar Guma ƙaurace wa gidajensu sakamakon hare-haren da ’yan bindiga ke kaiwa.
An sako limamin Katolika da aka sace a Kaduna An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a KanoWaɗanda aka kashen dai sun haɗa da: David Hur, shugaban shiyyar Cocin Anter Catholic da Misis Lydia Utuu ta ƙauyen Ayua.
Majiyoyi sun yi zargin cewa rikicin ya samo asali ne sakamakon wata arangama tsakanin wani makiyayi da wani mazaunin ƙauyen.
Rahotanni sun ce makiyayin ya yi yunƙurin wanke kansa ne a wata hanyar ruwa ɗaya tilo da al’umma ke da shi bayan ya sha daga ciki. Wani ɗan unguwar ya nuna rashin amincewarsa, wanda hakan ya haifar da rikici inda ake zargin makiyayin ya kai masa farmaki da adda.
“Mutumin ya yi neman agaji don jawo mutanen ƙauyen zuwa wurin, amma hargitsin ya kaure da sauri zuwa wani mummunan yanayi,” kamar yadda wani mazaunin garin ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho.
Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, mazauna yankin sun bar gidajensu da yawa. Har yanzu dai ana zaman ɗar-ɗar, tare da yin kira ga gwamnati da jami’an tsaro su shiga tsakani domin daƙile ci gaba da zubar da jini.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe, CSP Catherine Anene ba ta amsa tambayoyi kan lamarin ba don ƙarin haske a lokacin haɗa wannan rahoto.