Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno
Published: 7th, April 2025 GMT
Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari kauyen Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno, inda suka kashe sojoji tare da rasa mayaƙansu da dama.
Rahotanni na cewa harin ya auke ne da misalin karfe 1:00 na ranar Lahadi a lokacin da ’yan ta’addan suka mamaye sansanin sojin Nijeriya da ke garin Izge.
Wata majiyar tsaro ta tabbatar wa Aminiya cewar wani soji mai muƙamin Kyaftin da kuma Kofur na daga cikin waɗanda suka kwanta dama, yayin da sojoji suka yi nasarar hallaka mahara da dama a yayin arangamar.
Shugaban ƙaramar Hukumar Gwoza, Hon. Abba Kawu Idrissa Timta, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Sai dai ya ce har yanzu lokacin da aka tuntuɓe shi ba a kai ga tantance irin asarar da rayuka daga ɓangarorin biyu ba.
“Sai dai muna tabbatar da kashe ’yan ta’adda da dama,” a cewarsa.
Bayanai sun ce mahara da dama haye a kan babura sun mamaye sansanin sojojin, bayan da suka harba makamin roka da ake kira RPG a kansu.
Rahotanni sun ce, da farko sun kama hanyar nasara a kan sojoji, sai daga bisani mafarauta da ’yan banga suka ƙara ƙwarin guiwa har ta kai ga fatattakar maharan.
Majiyoyi sun ce sojoji da mafarauta da jajirtattun mazauna garin ne suka fatattaki ’yan ta’addan da ke tserewa zuwa dajin Sambisa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: jihar Borno mahara
এছাড়াও পড়ুন:
An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36
Da farko Kinjal Lathi, ta fara cire rai daga samun haihuwa da jin daɗin zama a matsayin uwa saboda cutar borin jini ta thalassemia da take fama da ita.
Dole a riƙa yi mata mata ƙarin jini duk bayan mako biyu, sannan dole ta bi wasu ƙa’idojin cin abinci da magunguna.
Mene ne matsayin azumin Sitta Shawwal a Mazhabar Malikiyya (2) ’Yan sanda sun gayyaci Sarki Sanusi domin amsa tambayoyiBayan kuma cutar da take fama da ita, akwai kuma ƙalubalen ɗaukar ciki da take fama da shi.
‘’Ina ganin fuskar ’yata sai na manta da duk wata wahalar da na sha a sanadiyar ɗaukar ciki da naƙudar,” in ji Kinjal Lathi, daga yankin Ahmedabad da ke Jihar Gujarat a kasar Indiya, inda ta ƙara da cewa, “ni da mijina mun sha kuka.”
“Akwai barazana babba ga uwa da abin da ke cikinta. Amma na yanke shawarar cika burina na zama uwa,” in ji Kinjal, kamar yadda majiyar BBC ta ruwaito.
Sai dai an yi wa Kinjal ƙarin jini sau 36 lokacin da take da ciki, amma kuma ta haifi lafiyayyiyar jaririya a ranar 12 ga watan Yulin 2019.
Ko bayan haihuwar ma, sai da aka ci gaba da yi wa Kinjal mai shekara 25 ƙarin jini, inda ta ce wasu lokutan ma ana yi mata ƙarin jinin ne a yayin da take shayar da jaririyarta.
Sannan kuma wani abun farin cikin shi ne ’yarta ba ta gaji cutar ba.
Wata ƙwayar halitta ce take samun matsala, wadda ke hana cuɗanyar jini da iska domin samar da jinin da ake kira haemoglobin, wanda shi ne yake zagayawa da jini mai ɗauke da sinadarin protein a jiki.
Yaya cutar thalassemia ke shafar juna biyu?
Ba a cika masu irin wannan cuta irin Kinjal suna haihuwa lafiya ba, kamar yadda likitan yara, Anil Khatri, wanda yake cikin kwamitin kar ta kwana na yaƙi da cutar ya bayyana.
Ya ce, bai taɓa ganin haka ba sama da shekara 30 da ya yi yana aikin kula da masu cutar ba, inda ya yi jinyar masu cutar sama da guda 100.
Akwai masu cutar kusan miliyan 270 a duniya, kamar yadda ma’aikatar lafiya da walwalar iyali ta bayyana.
Akwai na’ukan cutar da dama, ciki har da wadda ake kira ‘Hemoglobin H disease’, wadda ita ma ta kasu kashi biyu, wato nau’in alpha da beta – nau’in beta (TM) ce ta fi illa.
A Indiya akwai yara kimanin 100,000 zuwa 150,000 da suke ɗauke da cutar.
Ɗaukar ciki abu ne mai wahala ga mata masu cutar, kamar yadda likitan haihuwa, Umar Khatri ya bayyana.
Idan mace na da juna biyu, jininta yana ƙaruwa, wanda hakan ya sa jikin ke buƙatar ƙarin sinadarin ‘iron’ domin tallafa wa kai iska zuwa ga jariri.
“A ƙa’ida muna kiran mata masu juna biyu ne, su zo a duba su aƙalla sau ɗaya a wata.
“Amma ita Kinjal tana zuwa ne duk kwana 15, wanda shi ne karo na farko da muka samu hakan,” in ji Khatri.