Aminiya:
2025-04-07@14:27:27 GMT

Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC

Published: 7th, April 2025 GMT

Hukumar Yaƙi Da Cututtuka Masu Yaɗuwa a Nijeriya, NCDC ta ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon cutar sanƙarau a Nijeriya ya kai 151.

Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna ƙaruwar waɗanda suka kamu da cutar daga 74 zuwa 156 a jihohin ƙasar 23.

Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back

Jihohin da aka fi samun yawan mace-macen sun haɗa da Kebbi, da Sakkwato da Katsina da Jigawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Borno da Kano da Adamawa da kuma Oyo.

NCDC ta ce ta tabbatar da kamuwar wasu mutum 126 daga cikin mutum 1,858 da aka yi zargin suna dauke da cutar a jihohin ƙasar 23.

Wani rahoto da NCDC ta fitar a ranar Lahadi, ta ce jihohin Jigawa, Yobe, Gombe, Katsina, Adamawa, Kebbi da kuma Sakkwato su ne sahun gaba na masu fama da cutar a bayan nan.

Cutar Sanƙarau dai cuta ce da aka fi ɗauka galibi a lokacin zafi.

Wasu mutanen na iya yaɗa cutar ba tare da sun san suna ɗauke da ita ba, akasarin mutanen da ke ɗauke da ita ba su sani ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

Sudan: Ana Ci Gaba Da Yin Fada Tsakanin Sojoji Da Rundunar Daukin Gaggawa A Um-Durman

Sojojin Sudan suna ci gaba da bata-kashi da dakarun rundunar kai daukin gaggawa a yammaci da kudancin birnin Umdurman.

Majiyar gwamnatin Sudan ta fada wa manema labaru cewa; An dauke mazauna yankin da ake fadan a birnin Umdurman da adadinsu ya kai 5,000 zuwa arewacinsa.

A lokaci daya kuma sojojin na Sudan suna  ci gaba da abinda su ka kira da “Shara” a yankin “Jabalul-Auliya” dake kudancin birnin Khartum.

A can birnin Al-Fasha, jiragen saman sojojin Sudan suna kai hare-hare akan  wuraren dakarun kai daukin gaggawa a cikin birnin, da hakan ya haddasa asarar ta rayuka da kuma kayan yanki.

A cikin kwanakin bayan nan sojojin Sudan suna samun nasara akan dakarun kare daukin gaggawa da ya hada da korarsu daga birnin Khartum da wasu muhimman birane da su ka hada da Jazira.

Tun a cikin watan Aprilu na 2023 ne dai kasar Sudan ta fada cikin yakin basasa, bayan da dakarun rundunar kai daukin gaggawa su ka mamaye wasu cibiyoyin gwamnati.

 Ya zuwa yanzu dai adadin wadnada su ka rasa rayukansu sun wuce 20,000, yayin da wasu miliyan 15 su ka zama ‘yan hijira.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliya Ta Hallaka Mutum 30 A Birnin Kinshasa Na Jamhuriyar Demokradiyar Congo
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta
  • Trump Ya Yada Hutunan Bidiyo Wadanda Suka Nuna Yadda Sojojin Amurka Suka Kashe Mutanen Yemen Wadanda Suke Bukukuwan Salla Karama
  • An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36
  • An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe
  • Sharhin Bayan Labarai: Amurka Ba Zata Taba Zama Mai Kawo Karshin Yaki A Gaza Ba
  • Sudan: Ana Ci Gaba Da Yin Fada Tsakanin Sojoji Da Rundunar Daukin Gaggawa A Um-Durman
  • Adadin mutanen da suka mutu a girgizar kasa a Myanmar ya karu zuwa 3,354
  • Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu