Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC
Published: 7th, April 2025 GMT
Hukumar Yaƙi Da Cututtuka Masu Yaɗuwa a Nijeriya, NCDC ta ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon cutar sanƙarau a Nijeriya ya kai 151.
Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna ƙaruwar waɗanda suka kamu da cutar daga 74 zuwa 156 a jihohin ƙasar 23.
Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It BackJihohin da aka fi samun yawan mace-macen sun haɗa da Kebbi, da Sakkwato da Katsina da Jigawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Borno da Kano da Adamawa da kuma Oyo.
NCDC ta ce ta tabbatar da kamuwar wasu mutum 126 daga cikin mutum 1,858 da aka yi zargin suna dauke da cutar a jihohin ƙasar 23.
Wani rahoto da NCDC ta fitar a ranar Lahadi, ta ce jihohin Jigawa, Yobe, Gombe, Katsina, Adamawa, Kebbi da kuma Sakkwato su ne sahun gaba na masu fama da cutar a bayan nan.
Cutar Sanƙarau dai cuta ce da aka fi ɗauka galibi a lokacin zafi.
Wasu mutanen na iya yaɗa cutar ba tare da sun san suna ɗauke da ita ba, akasarin mutanen da ke ɗauke da ita ba su sani ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Ta Ce: Shugaban Rikon Kwarayar Siriya Al-Julani Ya Yi Alkawarin Cewa Ba Zai Cutar Da Tsaron Isra’ila Ba
A ganawarsa da wata jami’ar Amurka, al-Julani ya yi alkawarin ba zai cutar da tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ba!
Barbara Leaf, tsohuwar mataimakiyar sakatariyar harkokin wajen Amurka mai kula da harkokin gabas ta tsakiya, ta tabbatar da cewa shugaban rikon kwarya a Siriya, Mohammed al-Julani (al-Shara’a), “ya bayyana fahimtar matsalolin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila,” a cewarta.
Hakan ya zo ne a wata ganawa tsakanin Leaf da al-Julani a birnin Damascus, jim kadan kafin ta bar mukaminta. Leaf ta bayyana taron a matsayin “mai kyau kuma mai amfani.”
Har ila yau Leaf ta yaba da “hanzari da kuma dabarar da Shara’a ke bi wajen tunkarar al’amurran yankin,” tana mai cewa “yana neman kulla kyakkyawar alaka da bangarorin yankin.”