Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo ya kashe aƙalla mutane 30 tare da haddasa ɓarna mai tarin yawa.

Ruwan saman ya janyo tsaiko wajen gudanar da al’amura a babban birnin tare da katse zirga-zirgan ababen hawa a kan titin Kinshasa, wanda ya taso daga tsakiyar birnin zuwa filin jirgin sama.

A gundumar Debonhomme da ke gabashin ƙasar, ruwan ya laƙume motoci da dama, lamarin da ya tilastawa wasu mazauna ƙasar yin  hijira a yayin da wasu suka yi amfani da kwale-kwale kamar yadda jam’in kamfanin dillancin labaran AFP ya shaida.

Wasu daga cikin waɗanda abun ya shafa, sun maƙale a saman gidajensu bayan da ruwan ya mamaye matakalar shiga gidanjensu.

Bugu da ƙari, Ambaliyar ya haifar da cunkoson ababen hawa a birnin da ake fama da yawan zirga zirga.

Mazauna yankin da abin ya shafa sun shaidawa manema labarai cewa sun fusata bayan da gwamnati ta ƙi kawo musu agajin gaggawa.

 

rfi

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ambaliya

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 

Gwamna Caleb Mutfwang ya bayyana hare-haren baya-bayan nan da kashe-kashen da aka yi a wasu sassan jihar a matsayin shirin masu nufin tada zaune tsaye da kawo cikas ga zaman lafiyar jihar ne a maimakon a alakanta harin da rikicin manoma da makiyaya.

 

Da yake karin haske kan lamarin, Mista Aradong ya ce ‘yan bindigar sun kuma yi awon gaba da kayan abinci da sauran kayayyaki.

 

Mista Aradong, wanda ya yabawa gwamnatin jihar da jami’an tsaro bisa fara gudanar da binciken gaggawa da suka yi, ya kuma bukaci a kara tura jami’an tsaro a yankunan da lamarin ya shafa.

 

Da yake jawabi yayin ziyarar, Mista Jatau, wanda ya jajanta wa iyalan da suka rasa ‘yan uwansu yayin harin, ya kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta kuma bayar da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
  • Harin Filato: An kashe Mutane 40, An Kona Gidaje 383, Fiye Da Mutane 1,000 An Raba Su Da Muhallansu 
  • An Kori Jirgin Ruwan Japan Da Ya Shiga Yankin Ruwan Kasar Sin Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Gwamnatin Yobe Ta Ƙaryata Rahoton Bayyanar Boko Haram A Babban Birnin Jihar
  • An kai wa motar haya hari an kashe mutum 2 da sace wasu a Benuwe
  • Sudan: Ana Ci Gaba Da Yin Fada Tsakanin Sojoji Da Rundunar Daukin Gaggawa A Um-Durman
  • Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu
  • Saboda Rikicin Kasar Sudan Ta Kudu Shugaba Musaveni Ya Isa Birnin Juba
  •  Limamin Tehran: Babbar Jarabawar Dake Gaban Al’ummar Musulmi Ita Ce Kare  Al’ummar Falasdinu