Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 30 a Kongo
Published: 7th, April 2025 GMT
Ambaliyar da aka samu sanadiyar mamakon ruwan sama ta kashe aƙalla mutum 33 a Kinshasa, babban birnin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo.
Ruwan saman kamar da bakin ƙwarya ya janyo tsaiko wajen gudanar da al’amura a babban birnin tare da katse zirga-zirgar ababen hawa a kan titin Kinshasa, wanda ya taso daga tsakiyar birnin zuwa filin jirgin sama.
A gundumar Debonhomme da ke gabashin ƙasar, ruwan ya laƙume motoci da dama, lamarin da ya tilasta wa wasu mazauna ƙasar yin hijira.
Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito cewa wasu mazauna yankin na yunƙurin hijira ta cikin ruwa da ninƙaya, wasu kuma sun yi amfani da kwale-kwale.
Birnin na da mazauna miliyan 17, wanda ke da maƙotaka da kogin Kongo — ɗaya daga cikin mafiya girma a duniya.
Wasu ɓangarorin birnin na fama da zaizayewar ƙasa, abin da shugaban ƙasar ya ce sauyin yanayi na ƙara ta’azzara lamarin.
BBC ya ruwaito cewa ruwan ya share gidaje da yawa a yammacin Kinshasa ranar Juma’a zuwa wayewar garin Asabar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliyar ruwa Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo ruwan sama
এছাড়াও পড়ুন:
Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
Sojojin kasar Yemen sun yi amfani da jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa kan cibiyoyin makamai na HKI wadanda suka Yaffa (tel aviv) saboda daukar fansa kan kashe-kashen da take yi a Gaza.
Tashar talabijin Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran YAF na kasar Yemen yana fadar haka a jiya Jumma’a, ya kara da cewa sojojin yahudawan sun kai hare-hare kan unguwar Shaja’iyya inda suka kashe Falasdinawa da dama.
Ya zuwa yanzu tun fara yakin tufanul Aksa, a cikin watan Octoban shekara ta 2023, falasdinawa kimani 51,000 sannan wasu 115,688 a gaza. Ta kuma rusa kimani kasha 90% na gine-ginen Gaza.