Arakci: Amruka Tana Mafarkin Kulla Yarjejeniya Da Iran Kwatankwanci Wacce Ta Yi Da Kasar Libya
Published: 7th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Sayyid Abbas Arakci ya bayyana cewa, Iran ba ta kin zama teburin tattaunawa, amma ba za ta zauna gaba da gaba da Amurka ba, yana mai kara da cewa; Har ya zuwa yanzu ba a yi wata tattaunawa gaba da gaba a tsakanin Iran da Amurka ba.
Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya gabatar da jawabi a gaban kwamitin siyasar waje na majalsar shawarar musulunci ta Iran ya gabatar da rahoto akan hali na karshe da ake ciki dangane da batun tattaunawa da Amurka.
Arakci ya kuma fadawa kwamitin cewa; Mu ma’abota diflomasiyya da tattaunawa ne, amma za mu tattauna da Amurka ne ba kai tsaye ba,kuma duk da hakan ma har yanzu ba mu bude tattaunawa ba.”
Wani daga cikin ‘yan kwamitin ya tambayi Araki akan ko Amurka tana tunanin kulla yarjejeniya da Iran irin wacce ta yi da Libya a 2003?
Arakci ya ba shi jawabi da cewa; Abu ne mai yiyuwa mafarkin da suke yi kenan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito
Gwamnatin kasar Sin ta yi kakkausar suka da bayyana adawarta ga matakin Amurka na kakaba “harajin fito na ramuwar gayya.”
A cikin wata sanarwar da ta fitar, ta yi Allah-wadai da matakin na Amurka, wanda ya kasance daukar mataki bisa radin kai, da kuma kariyar cinikayya da cin zarafin tattalin arziki.
Sanarwar ta kara da cewa, ta hanyar fakewa da abin da take kira “ramuwar gayya” da “adalci,” a zahiri dai Amurka ta tsunduma a aiwatar da dabarun danniya da babakere, tana neman cimma manufarta ta “Amurka na gaba da komai” da kuma “Amurka ta fi kowace kasa.” Har ila yau, Amurka na amfani da harajin fito don kawo cikas ga tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa, tare da fifita muradun Amurka sama da moriyar bai daya ta duniya, tare kuma da sadaukar da halaltattun muradun kasashen duniya don cimma burin Amurka.
A ranar Laraba ne dai shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da wani sabon tsarin haraji, inda ya sanya mafi kankantar harajin fito kashi 10 cikin dari kan kayayyakin da ake shigowa da su daga dukkan kasashe abokan huldar cinikayyarta da kuma karin sama da hakan kan waasu kasashen. Bayan matakin na Amurka, a ranar Juma’a kasar Sin ta sanar da cewa, za ta sanya karin harajin fito kashi 34 cikin dari kan dukkan kayayyakin da ake shigowo da su daga Amurka daga ranar 10 ga watan Afrilu, wanda ya yi daidai da harajin fito na ramuwar gayya da Amurka ta kakaba kan kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin.
A cikin sanarwar da gwamnatin kasar Sin ta fitar yau Asabar ta ce, kasar Sin ta dauki kuma za ta ci gaba da daukar kwararan matakai don kiyaye ‘yancinta, da tsaro, da muradunta na samun ci gaba.